Thursday, November 10, 2016

Musulmai sun shiga wani hali bayan Trump yaci zabe

Zaben Donald Trump: Musulmai suna ta Lahaula


Musulman duniya sun rikice bayan da Donald Trump ya samu nasara a zaben Kasar Amurka

 


Musulmai na tsoron za ayi ta kashe su a duniya

 


Donald Trump yayi alkawarin hana Musulmai shiga Kasar Amurka

 

Syed Chowdhury, wani Musulmi dan Kasar Bangladesh yace Amurkawa sun ja wa duniya bala’i, watau da suka zabi Donald Trump Shugaba. Musulmai fiye da Biliyan daya a duniya suna tunanin yadda abubuwan za su kasance bayan da Donald Trump ya lashe zaben Kasar Amurka.

Wata Baiwar Allah ta ke cewa ‘Ya ‘yan ta ka da su kara saka Hijabi daga yau, tun da Donald Trump yaci zabe. Wani yake cewa bai san yadda ‘Yan Gidan su za su yi ba. Alijah Diete, wani dan gwagwarmaya daga Indonesia yake cewa: ‘Ina tsoron za a shiga Yaki, Amurka tayi ta kashe mutane na Kasashen Musulmai

Wani Farfesa, Zuhairi Misrawi yace babu wadanda za su fi kowa murnar nasarar Trump, sai ‘Yan ta’adda na Kungiyar ISIL. Ishaq Khan yace ya so ace Hillary Clinton ce taci zabe, da Pakistan ta zauna lafiya. Khan yace Donald Trump fada da Musulmai zai yi, ban ji dadi da yaci ba. A Garin Dubai ma dai, duk mutanen na cikin wani yanayi na lahaula, bayan da aka ce Trump yaci zabe.

A gida Najeriya  kuma, Farfesa Wole Soyinka yace Najeriya da sauran Kasashen Afrika musamman na Yamma ba za su rika samun irin taimakon da suka rika samu a lokacin Shugaba Barrack Obama ba. Minista Audu Ogbeh yace Sabon Shugaban Kasa Donald Trump dan jari-hujja ne, zai kuma kashe Kasar Amurka. Shi kuwa Ministan Tsaro na Kasar, Birgediya-Janar Mansur Dan-Ali mai ritaya, cewa yayi dole a rungumi kaddara.













No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...