Hudubar Juma’a daga Mimbarin ITN-Zaria
-Tambayoyin Kabari’-Daga Bakin Imam Ustaz Sa’eed Yunus.
Assalamu Alaikum wa Rahmatul Lah,
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah SWT, tsira da amincin Allah su tabbata ga wanda babu Annabi
bayan sa, Shugaban mu, kuma Annabin mu, farin Jakadar Allah; Annabi Muhammadu
SAW, tare da iyalan sa da Sahaban sa tare da duk wadanda suka bisa da
kyautatawa zuwa har Ranar karshe.
Bayan haka, ‘Yan uwa mu ji
tsoron Allah. Lallai babban guzuri ga bawa shi ne tsoron Allah. Ubangiji ya
fada cikin Suratul Nisa’i a Al-Kur’ani mai girma cewa: ‘Lallai mun yi wasici ga wanda muka ba littafi, da wadanda suka zo kafin
ku, da ma ku kan ku da ku ji tsoron Allah’
Hudubar yau tana mana ne magana
game da tambayoyin cikin kabari. Tabbas, bayan mun bar wannan duniya, za a
bijiro mana da tambayoyi a cikin kabari wanda Allah ya rubuta. Hatta wanda ba a
birne ba, sai anyi masa wadannan tambayoyi.
‘Yan uwa sababi na mutuwa
suna da yawa a yau, wasu mugaye su kan kashe mutum. Annabin Rahama SAW kuwa
yayi gaskiya, yace karshen zamani, za a samu wasu masu kashe mutane, su wadanda
suka yi kisan ba su san dalilin da ya sa suka yi ba, haka wanda aka kashe bai
san abin da yayi aka kashe sa ba. Allah ka tsare mu.
‘Yan uwa babu wanda zai
rasu, Musulmi ko wanin sa, face sai an dawo masa da ran sa a jikin sa daga
lokacin da ‘Yanuwan sa su ka bar wurin bizne sa. Amma kai idan ka ga kabarin,
sai kace ya abin zai yiwu? Allah kuwa ya tsara haka, ya kuma ba Mala’ikun nan
biyu umarnin su tambayi bawa.
Za a tambayi bawa abubuwa kamar
haka: Wanene Ubangijin ka? Menene addinin ka? Wanene Annabin ka? Sannan ya ka
san Allah? Bawa na kwarai zai amsa da cewa Ubangiji na shine Allah. Annabi na
kuma shine Annabi Muhammad SAW. Addini na Islam kuma shine Addini na. Sai ace
da shi ta ya ka gane wadannan, sai bawa yace na karanta littafin Allah, Al-Kur’ani.
Na gaskata Manzon tsira SAW. Wannan Bawa ya samu cin jarabawa.
Duk wanda ya karanta Al-kur’ani,
Ubangiji yana cewa: ‘Ubangijin ku shine
Allah…’, kuma yake cewa: ‘Muhammadu
SAW, manzon Allah ne…’, Sannan kuma duk wanda ya ke karatun Al-Kur’ani ya
san cewa: ‘Addini a wajen Allah, shine
musulunci’. A takaice, zai amsa wannan tambayoyi kuma za a bada sakamakon
wannan jarrabawa da kuma kyaututtuka guda 6; Na daya; Za ayi masa shimfida da
mashinfidin Aljanna. Na biyu; Za a masa tufafi da tufafin Gidan Aljanna. Na uku:
Za a budewa wannan Bawa wata kofa da zai rika shakar iskar Gidan Aljanna. Za
kuma a nuna masa arzikin sa na duniya. Na hudu: Za ayi masa bushara da Aljanna
tun a kabari. Na biyar: Allah SWT zai yi umarni a buda ma Bawan kabarin sa, ya
zama mai fadi. Na shida kuma: Ubangiji zai saka haske cikin kabarin. Wannan ya
zo a cikin Hadisin Sahabi Barra’ RA a cikin Sunan Tirmidhi.
Babban Maruwaici, Abu
Hurairah RA yake cewa a wata ruwayar daga Tirmidhi. Allah kara masa yarda,
cewa, Ana saka haske a cikin kabarin Bawa na gari. Sannan a cikin kabarin, Bawa
zai ga wani mutum kyakkyawa mai kanshin jiki da sura yana masa sallama da busharar isowa, ko idan
bawa ya tambaye wanene wannan mai matukar kyawun sura, sai yace ni ne ayyukan
ka na Gidan .
A takaice saboda
wannan hadisi, sai muyi aiki mai kyau. Za a fitar da mutum daga gidan sa ana
kuka, alhali yana hangen alherin da zai fuskanta gaba. ‘Yan uwa aiki ya gan mu;
maza da mata. Manya da kanana. Akwai morewa ga wanda Allah ya sa suna da rabo.
Bangare na 2 na huduba
Bayan godiya ga Allah SWT da
yabo ga farin jakadan Annabi Muhammad SAW. Mu ji tsoron ranar da za mu koma
kabari. Mu sani cewa kabari gaskiya ne, wasu mutane sun munana ayyukan da za su
gani a kabari; wasu sun zama masu ha’inci wajen aiki da sana’a. Gulma da zunde
ya zama aikin wasu, wasu sun zama annamimai. Wasu suna aikata abin da Allah ya
hana, wasu kuma suna yada sharri, duk wanda ya yada sharri, zai iske sharri a
lahira. Jama’a suna yada cewa akwai yunwa a Kasar mu, Allah ya raba mu da yunwa.
Babban Sahabi Ibn Umar RA yace: ‘Idan danuwan ku ya rasu, idan na kirki ne, zai
ga farin ciki a kabarin sa. Idan kuma na banza ne, zai ga bakin ciki.’ Allah ka
kare mu.
Za ayi wa kowa wadannan
tambayoyi, kamar yadda aka ambata. Idan dan wuta ne; za a yi masa tufa daga
cikin kayan wuta. Za kuma a bude masa kofa daga cikin na Jahannama mai hurowa
da zafi. Duhu zai cika kabarin sa har sai Ranar da aka yi busar Kiyama. Ubangiji
Ta’ala SWT zai yi umarni da a kara kuntata kabarin wannan Bawa ya zama babu
yalwa, daga karshe kuma ayi masa bushara da wutar Jahannama. Allah ka tsare mu.
Amin.
Don Allah me ya kamata mu
zaba? Yanzu muke da rai. Babu wanda ya san abin da zai faru gare sa nan da zuwa
Jumu’a ta gaba. Ya mu’amalar ka da iyalin ka? Abokan ka? Da sauran Jama’a. Allah ya sa mu dace.
Allah ka buwaiyar da Addinin
Musulunci ka kaskantar da kafirci. Allah ka azurta mu, ka bamu zama lafiya a
Kasar mu. Allah ka kare mu daga azabar kabari, Allah kar fitinar da mu da kabari
ka tabbatar da harshen mu a cikin kabari.
[Sheikh Dr. Saeed Yunus]
Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga
Masallacin I.T.N-Zaria.
Twitter:@Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment