Tuesday, November 15, 2016

Wasu iyaye sun yi wa Donald Trump takwara


Wasu iyaye sun saka wa ‘Dan su da suka haifa suna Donald Trump


Mahaifin yaron yace yana matukar kaunar sabon shugaban Kasar Amurka


Wannan abu ya faru ne a Kasar Kenya

 

A Kasar Kenya wani abun al’ajabi ya faru inda wasu iyaye suka saka wa dan suka haifa sunan sabon Shugaban Kasar Amurka, Donald Trump. Wadannan iyaye sun yi sabon Shugaban Kasar Amurka Donald Trump takawara saboda tsabar soyayya.

Jaridar Daily Nation ta Kasar Kenya ta rahoto wannan labara. Iyayen wannan yaro sun ce Donald Trump yana matukar burge su. Mahaifin wannan ‘da yace shi musamman akidu da manufafofin wannan mutumi watau Donald Trump yana ba sa sha’awa kwarai da gaske. 

Mista Felix Otiano ya sakawa dan sa da haifa kwanaki dai suna Donald Trump. An sakawa wannan yaro sunan Donald Trump ne tun ma kafin takwarar na sa ya san zai lashe zaben Shugaban  Kasar Amurka. Mista Felix, Mahaifin wannan ‘da yace Donald Trump ya cancanci zama Shugaban Kasar Amuka.

Wannan abu dai ya kawo ce-ce-ku-ce a Kasar, shi dai mahaifin yace ba don ya zama Shugaban Kasa ya masa takwara da dan cikin sa ba. Kwanakin baya, Farfesa Wole Soyinka yace Najeriya da sauran Kasashen Afrika ba za su rika samun irin taimakon da suka rika samu a lokacin Shugaba Barrack Obama ba tun da Donald Trump ya zama sabon Shugaban Kasar Amurka.

Donald Trump ya buge Hillary Clinton 'Yar takarar Jam'iyyar Democrat a zaben da aka kammala wancan makon na Kasar Amurka.

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...