Wednesday, November 2, 2016

Gwamnatin Shugaba Buhari za ta kirkiro sababbin Jami’o’i

Gwamnatin Shugaba Buhari za ta amince da kirkiro sababbin Jami’o’i a fadin Tarayyan Kasar

 


Duk Jami’o’in da za a karo na kasuwa ne, ba na Gwamnati ba

 


Gwamnatin Tarayya ta yanke wannan shawarar ne a zaman da ta yi na yau

 



A zaman Majalisar zartarwa na Tarayyar Kasar watau FEC na Yau, Gwamnatin Shugaba Buhari ta amince da kirkiro sababbin Jami’o’i a fadin Kasar nan har guda 8. Gwamnatin Shugaba Buhari ta dauki wannan mataki ne a zaman Majalisar zartarwa na mako-mako da tayi a Fadar Gwamnati da ke Birnin Abuja.

A taron da aka yi a Aso Rock, Gwamnatin Shugaba Buhari tayi na’am da karo sababbin Jami’o’i guda 8 a fadin Najeriya. Sai dai kaf wadannan Jami’o’i bana Gwamnati bane, watau na ‘yan kasuwa ne.


Shugaba Buhari ya jagoranci wannan taro da shi da Ministocin sa tare da sauran mukarraban Gwamnatin Tarayya. Sababbin Jami’o’in sune; Jami’ar Anchor a Legas, Jami’ar Clifford, Jami’at Coal City, Jami’ar Dominican, Jami’ar Kola Daisi, Jami’ar Legacy dsr. 

Haka kuma a yau Kungiyar Kwadago ta Kasa watau NLC, za ta zauna da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari. Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zai gana da Kungiyar Kwadago ta Kasa NLC, da kuma Kungiyar ‘Yan Kasuwan Najeriya watau TUC domin ganin Shugaba Buhari ya kara albashin ma’aikata daga N18000 zuwa akalla N56000 a kowane wata.

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...