Friday, November 25, 2016

Atiku Abubakar ya cika shekaru 70

An taya Atiku murnar zagayowar Ranar haihuwar sa

– Tsohon mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar ya cika shekaru 70 da haihuwa

 

– Jam’iyyar APC ta taya Atiku murna, tace sune Najeriya

 

– Tsohon mataimakin Shugaban Kasan yayi hidima wajen inganta rayuwa da siyasar al’umma

 


Tsohon mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar ya cika shekaru 70 a duniya, Jam’iyyar su ta APC ta taya sa murnar wannan rana. APC tace ba zai yiwu a rubuta Tarihin Najeriya ba tare da sunan Atiku ba. 

APC tace Atiku Abubukar ya inganta rayuwar ‘Yan Kasar nan ta fannin mu’amala, zaman siyasa, tattalin arziki da cigaban al’umma. APC tace Atiku mutum ne wanda aba ruwan sa da bambancin kabila ko yare.

A sakon taya Atiku Abubakar din murnar zagayowar Ranar haihuwar sa, Jam’iyyar APC ta roka masa karin shekaru cikin koshin lafiya da arziki, Shugaban Jam’iyyar ne dai ya aika da wannan sako. APC tace alherin Atiku ya taba kowa a Kasar nan.

Haka kuma dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya taya Atiku Abubakar din murnar zagayowar wannan rana ta haihuwar sa, Shugaba Buhari ya taya Atiku shigowa sahun ‘Yan Saba’una irin sa.


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...