Tuesday, November 15, 2016

Mu muka kashe Abu Ali-Shekau


Shekau ya fito, yace su suka kashe Abu Ali


Ni na kashe Lt. Col. Muhmmad Abu Ali-Inji Shekau


Shugaban Bangaren Kungiyar Boko Haram, Shekau ya fito a wani sabon kaset


Abubakar Shekau yace shi ya kashe Babban Sojin Najeriyar nan, Muhammad Abu Ali


Shekau yace kadan ma kenan…

 

Abubakar Shekau, Shugaban wani bangaren Kungiyar Boko Haram ya fito a wani sabon kaset inda yayi jawabi cewa shi ya kashe Babban Jami’in Sojin Najeriyar nan watau Laftana Kanar Muhammad Abu Ali. An kashe gwarzon ne a Ranar 4 ga wannan watan na Nuwamba a Garin Malam Fatori da ke Borno.

A wani jawabi da ya samu kaiwa ga Jaridar Sahara Reporters, Shekau yace sune suka aika da Babban Sojin lahira, duk da bai fadi ainihin sunan jarumin ba. Abubakar Shekau din yace Bangaren sa na Kungiyar Boko Haram din ne ke kai duk wasu hare-hare da ake ji kwanan nan ga Sojojin Najeriyar. 


Abubakar Shekau yace yanzu ma aka fara, wasu hare-haren na nan tafe. Shugaban wani bangaren Kungiyar na Boko Haram yayi kaca-kaca da Sarkin Kasar Saudiya bayan ya taya Sabon Shugaban Kasar Amurka mai jiran-gado murna. 

Abubakar Shekau yace za su koma kan Donald Trump har sai sun ga bayan sa, da zarar sun gama da Shugaban Kasa mai ci na yanzu watau Barrack Obama. An dais ha cewa an kashe Shugaban na Boko Haram, Abubakar Shekau. A kwanakin baya Kungiyar ISIL ta nada wani a madadin sa a matsayin Shugaban Kungiyar Boko Haram din

Laftana Kanar Abu Ali ya kasance jarumi wanda ya nuna bajinta wajen kawar da Boko Haram daga Yankin Borno da Adamawa. Hakan ta sa aka kara masa matsayi daga Manjo zuwa Laftanar Kanal din tun a shekarar da ta wuce. An kashe sa tare da wasu Sojoji 6 a Farkon wannan Wata.



KU KARANTA LABARAI A SHAFIN MU NA NAIJ HAUSA



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...