Muna nan, sai mun gyara Kasar nan-Shugaba Buhari
– Shugaba Buhari yace duk mai shirin barin Najeriya, ya sauka lafiya
– Shugaba Buhari yace amma fa su suna nan, babu inda za su je, sai Najeriya tayi kyau
– Shugaban Kasa ya fadi hakane lokacin da ya gana da Shugabannin Neja-Delta
Shugaba Buhari yace duk
wanda yake ganin yana da wurin zuwa da ba Najeriya ba, to sai yayi tafiyar sa,
ya sauka lafiya, amma fa su suna nan har sai sun gyara Najeriya. Mai magana da
bakin Shugaban Kasar, Mallam Garba Shehu ya bayyana wannan jawabi na Shugaban
Kasar.
Shugaba Buhari yayi wannan
magana ne a lokacin da ya gana da Shugabannin Yankin Neja-Delta a jiya. An yi
wannan tattaunawa domin ganin an samu wanzuwar zaman lafiya a Yankin na
Neja-Delta. Shugaba Buhari yake cewa duk wanda yake da wata Kasa da ba Najeriya
ba, sai ya fice, ya tafi can.
Shugaba Buhari kuwa yake
cewa za su tsaya a Kasar har sai sun gyara ta, Shugaban Kasar ya koka da irin
halin da ake ciki; yake cewa har ta kai Jihohi da dama ba su iya biyan albashin
ma’aikatan su.
A Karanta cikakkun labarai a NAIJ Hausa
No comments:
Post a Comment