Tuesday, November 29, 2016

Abubuwa 10 da ya kamata ka sani game da Fidel Castro


– Tsohon Shugaban Cuba Fidel Castro ya bar duniya Ranar Jumu’a

 

Fidel Castro ya rasu yana da shekaru 90

 

Tsohon Shugaban ne ya jagoranci juyin juya-halin da aka yi a Kasar Cuba shekaru 50 da suka wuce

 

Shin Wanene Fidel Castro?

 

 Castro kenan yana busa karar sa 'yar gida

Yayin da ake zaman makokin Fidel Castro a Kasar Cuba. Mun kawo maku dan takaitaccen Tarihin sa.

  •  An haifi Fidel Castro a shekarar 1926, a Garin Oreiente da ke Yammacin Kasar Cuba

  • An daure Fidel Castro a shekarar 1953 bayan yayi yunkurin kifar da Gwamnati

  • A shekarar 1955 aka saki Fidel Castro daga Gidan Yari

  • A shekarar 1959 ya samu kifar da Gwamnatin Shugaban Kasar lokacin, ya zama Shugaba

  • A shekarar 1961 ya yaki harin da wata Kungiya da CIA ta Amurka ta marawa baya ta kawo masa
  •  
  •  A shekarar 1976 Majalisar Kasar Cuba ta zabi Fidel Castro a matsayin Shugaban Kasa

  • A kuma shekarar 1976 ya kulla yarjejeniya da Kasar Amurka  game da ‘Yan gudun Hijira

  •  A shekarar 2006 ya sauka daga Shugabancin Kasar Cuba 

  • Dan uwan sa Raul Castro ya gaje sa
  •  
  • Fidel Castro ya mutu a shekarar 2016 yana mai shekaru 90 a duniya. 

[BBC]




Jami’ar ABU Zaria ta yaye dalibai 11,000

An yaye daliban ABU Zaria


Jami’ar ABU Zaria ta yaye dalibai sama da 11,000 a karshen wannan makon

 


Jami’ar ta yaye dalibai masu digiri da digirgir har ma da digir-digir

 


Ciki an samu guda 49 da suka ciri tuta

 

 Shugaban Jami'a, Farfesa Ibrahim Garba

Jami’ar Ahmadu Bello watau ABU Zaria ta yaye dalibai a karshen wannan makon. Jami’ar da ita ce ta farko a Arewacin Najeriya ta yaye dalibai masu digiri guda 11, 731. 

Kamar yadda muka samu labari akwai guda 2, 697 masu shaidar Digiri na biyu, sannan kuma guda 289 sun kammala karatun Digiri na uku watau Dakta. Ciki akwai guda  49 da suka ciri tuta, inda suka samu gamawa da mataki na farko watau 'first class'.

Shugaba Buhari ya ce za ayi bincike game da irin badakalar da ake samu a cikin Jami’o’i. Shugaban Kasar ya kuma yi kira da Jami’ar ta ABU Zaria da ta maida hankali wajen nazari game da harkar noma. Farfesa Rasheed na Hukumar NUC ne ya wakilci Shugaban Kasar. 

Shugaban Jami’ar Farfesa Ibrahim Garba ya bayyana irin cigaban da Jami’ar ta samu wajen fanni dabam-dabam a karkashin Shugabancin sa. ABU Zaria ta gina matatar man fetur, sannan kuma ta gano wani maganin cutar malaria na ciwon sauro.

Farfesa Garba ya kira daliban da aka yaye su zama masu tarbiya bayan ilmin da suka samu. Yanzu haka Jami'ar ABU Zaria ta yaye dalibai da dama a fadin duniya. Wannan ne dai karo na 39 da Jami'ar ta yaye daliban nata.




Muhammad Malumfashi daga Zaria
NAIJ Hausa

Monday, November 28, 2016

Shekarar su 10 suna soyayya, yanzu za su yi aure

Tsuntsayen soyayya




– Ola Moses zai auri Temi bayan sun kwashe shekara-da-shekaru suna soyayya

 


– Shekarar tsunstayen goma suna soyewar su


Kamar dai yadda Hausawa kan ce: Abu karamar wasa, karamar magana ta zama babba…Wadanna bayin Allah sun shafe shekaru fiye da goma suna tare, ga shi Allah yayi za su kuma yi aure. 

Kamar yadda Sahibar ta fada, Temi tace tun shekarar 2006 suka hadu a Coci wajen bauta, Moses ya kuwa tambaye ta lambar waya, nan take ta mika masa. A wancan lokaci ana yayin waya kyauta da tsakar dare… Shekaru goma kenan, ga shi yau, za suyi aure. 

Timi tace kafin sa, ba ta taba soyayya a duniya ba, kuma shine na karshe. Timi tace Moses ya nuna mata yadda ake soyayya a rayuwa, kuma da shi kadai ta taba yi. Timi tace lokacin da Ola Moses ya tafi Kano, ta zaci ba zai dawo ba. 

Suka ce an ta kokarin a ga bayan su a rayuwa, sai dai Ubangiji ya kaddara za su auri juna. Tace har jina-jina iyayen ta sun taba yi mata, amma ya zama Tarihi.




Kai kadai na rike a raina, kaunar ka nike yabawa... Allah ya hada Temi da Moses.



Ashe dama tusa na magani?

Tusa na maganin cutar tsufa
 

Bincike ya nuna cewa tusa na maganin cututtuka da dama

 


Turawa sun gudanar da wani bincike inda suka gano cewa tusa na maganin cututtukan tusfa

 


Iskar tusa tana rage kamuwa da cutar hawan jini da ire-iren su


A wani sabon bincike na kwanan nan, an gano cewa tusa na magani na cututtuka kala-kala. A baya dai ana tunanin cewa iskar tusa na da mugun illa, sai dai yanzu nazari ya nuna ashe ba haka abin yake ba. Tusa na maganin cuta duk da mafi yawan tusa, sai ka ji ta da dan-karan wari.

Masana sun gano cewa a duk lokacin da kayi tusa, ka kuma shaki iskar, to tana da amfani a jikin Dan Adam. Iskar tusa na hana kamuwa da cutar dementia ta tsufa. Cutar dementia na sa yawan mantuwa da dimuwa ga tsofaffi. Idan ana shakar warin tusa, wannan cuta ba za ta kama mutum ba. 

Wasu Turawan Birtaniya ne dai suka gano cewa, tusa na dauke da Iskar Hydrogen Sulphate. Masana kimiyya sun ce wannan iskar na da amfani a jiki mutum, musamman a kwakwalwa. Hydrogen Sulphate na karawa kwakwalwa karfi kuma tana kare mutum daga cutar tsufa. 


Muhammad Malumfashi ya fassara
NAIJ Hausa

Sunday, November 27, 2016

An karrama Shugaban NUC, Farfesa Rasheed


Kungiyar 'Kaduna Project' ta Zariya ta karrama Sakataren Hukumar NUC, Farfesa Abubakar Adamu Rasheed
 

Yariman Zazzau, Mannir Jafaru ya basa kyautar jinjina

 

An nemi Shugaban NUC din da ya rike gaskiya da adalci  

 


A wani taro da Kungiyar Kaduna Project ta gudanar, Kungiyar ta karrama sabon Sakataren Hukumar NUC ta kuma taya sa murna. An kuma kira sabon Sakataren Hukumar NUC din da ya zama mai gaskiya da adalci.
 
Kungiyar ta Kaduna Project da ta ke kamar cibiya ta Musulunci, ta taya Farfesa Abubakar Rasheed murnar samun wannan matsayi na Shugaban NUC. Kungiyar ta kuma taya Farfesa Umar Ibrahim murnar nada sa Shugaban laburare na Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. A taron kuma dai, an karrama Shugaban Asibitin Koyon aiki na Jami’ar da ke Shika, an kira Shugabannin da suyi kokarin rike amana.

Shugaban taro a tsaye, Alhaji Falalu Bello, Tsohon Shugaban Bankin Unity

An taya 'Ya 'yan Jihar murna da kuma neman su da su zama masu gaskiya da rikon amana. Farfesa Rasheed wanda asalin ‘Dan Garin Makarfi ne na Jihar Kaduna, ya zama Shugaban Hukumar NUC mai kula da Jami’o’in Kasar nan a watan Agusta. Farfesa Rasheed tsohon Shugaban Jami’ar Bayero ta Kano ne.

Shugaban Kungiyar NIC, Amir Muhammad D. Muhammad ya kira Farfesa Rasheed ya rike gaskiya da amanar al’umma, ya zama mai amfani da basirar sa, ya kuma san cewa Ubangiji zai tambaye sa a Ranar Kiyama. 

Farfesa Rasheed tare da Yariman Zazzau, Alhaji Mannir Jafaru da Uban Taro Alhaji Falalu Bello, Dan Masanin Zazzau


Farfesa Abubakar Adamu Rasheed yayi godiya ya kuma tabbatar da kamanta gaskiya a duk inda yake. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Mai Girma Yariman Zazzau, Mannir Jafaru da kuma Dan Masanin Zazzau, Falalu Bello da Farfesa Abubakar Sani Sambo da kuma wasu Manyan Malaman Jami’a da Shugabannin Al’umma. 


Muhammad Malumfashi daga Zaria
NAIJ Hausa


Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...