Wakar Mutuwa; Muhammad Malumfashi
Mutuwa
daya ta,
Sanadi
a' kala-kala,
Kabari
kowa da nasa,
Tambaya
dole ka amsa,
Idan
kayi gardama, ko kaci jibga,
Munkar-Nakiru
na nan, masu guduma,
Ban
da maciji, ga kunama,
Daga
barzahu, sai Kiyama,
Filin
tonon silili da gaskiya,
Ranar
da babu karya,
Kowa
na tube, Iko sai ga Jalla,
Ko
ka ga Sarkin kasar ku? Yana nan haihuwar uwar sa,
Can
a samu Muhammadu (SAW) ya roko alfarma,
Bayan
yayi kirari ya jinjina ma Tabara,
Sai
Hisabi awo na mizani, babu cuta,
Kowa
na ta kan sa,
Idan
ka cuce wani ne sai a rama,
A
diba ladan ka duk a ba sa,
Idan
babu ladar dada, zunubi nasa sai a dibo a jibga,
Babu
ruwan uwa da danta,
Ko
wani miji da yar matar sa,
Sai
dai bawa da ayyukan sa,
Gidaje
biyu, Aljanna ko wutar ubangiji Ta'ala
An
ce Allaah kadai ya san namijin kabewa,
Fatar
mu ace takarda a hannun dama an ka mika,
Mai
hannun hagu sai ka ji yana, ai mu har yanzu da saura jama'a,
Allah
kiyaye bawa da jahannama,
Ranar
wuta tana ta kugi, za ta fusga,
Mummuna
ce baka, don azaba,
Ita
ko aljanna, gidan ni'ima don a wala,
Allah
ya samu cikinta,
Ni
ko dan matan cikin ta,
Ga
koramu na ta gudana
Ga
giya sai mu taba, ni yar 'Star' babba za ni kurba,
Ba
wani bawali, ba zagayawa,
Ba
a koshi, kuma babu yunwa,
Da
ka yi marmari sai a ba ka,
Karshe
zad dadi sai a ga Allah ta'ala,
Can
wuta ko, ko ruwa ka nemi a ba ka,
Na
kwata ne, ga zafi ya dalma,
Ya
huda makwogwaron, don tafasa,
Ga
doyi, wari ba a ma magana,
Ina
ma abinci, mai huda tumbin yan Jahannama,
Ga
shi ba dama a koma duniya,
Ko
ace an mutu don a huta,
Siradi
muminai za su tsallaka,
Wani
kamar walkiya, wani kamar ya fada,
Da
kyar na sha ai yafi da kyar aka kama,
Allah
dai ya sa abin ya zo da sauri ya kiftawa,
Ran
sarki ya dade, ai ba ya hana Mutuwa,
Ga
mai nakuda, ta zo za ta haihu, ran aka dauka,
Jinjiri
ya leko, uwar sai ta koma,
Haka
yar kanwata Amina, yanzu sai ace marigayiya,
Ba
ruwan mutuwa da wai ko karama ce,
Shege!
Cinnaka, ba ka san na gida ba,
Wata
rana iyayena za ta dauka,
Allah
ya jikan su ya sa su huta,
Allah
kai ni Madina nima,
In
mutu can ina mai Salla,
Masallacin
shugaban mu nayi sujuda!
امين
Twitter:
@ya_waliyyi
Amin, Amin Amin abokina... cinnaka bai ma adalci ba hala! Lol
ReplyDeleteBa ruwan sa...
ReplyDelete