Saturday, October 22, 2016

Ganduje, Ka cire mana jar hular mu-Kwankwasiyya



‘Yan Kwankwasiya sun ce za su kai Ganduje Kotu idan bai cire masu hula ba


 

– ‘Yan Kwankwasiyya sun kira Gwamna Abdullahi Ganduje da ya tube masu Jar hula ko kuma su kai sa Kotu

 


Kwankwasiyya sun ce Ganduje ya bar akidar don haka babu dalilin  cigaba da zama da alamar su

 


Rikicin Ganduje da Tsohon mai gidan na sa Kwankwasiyya na ta kara cabewa

 

 

 


A jiya DailyTrust ta rahoto cewa magoya bayan Tsohon Gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ‘Yan kwankwasiyya’ sun nemi Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kanon da ya tube jar hular da ke kan sa, idan ba haka ba kuma za su shiga Kotu da shi nan da kwana biyu.


‘Yan Kwankwasiyya sun ce Gwamna Ganduje ba ya tare da su cikin tafiyar, don haka babu dalilin cigaba da saka jar hular Kwankwasiyya. A jiya ne dai Tsohon Gwamnan Kano kuma Shugaban tafiyar Kwankwasiyya Amana Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya cika shekaru 60 a duniya.


Haka kuma tafiyar Kwankwasiyya ta cika shekara 6 kenan a duniya, a wajen bikin murnar cika shekarun Tsohon Gwamnan kuma jagoran tafiyar ne wani mabiyin Kwankwasiyya, kuma Shugaban Hannun karba-Hannu badawa, Alhaji Sharu Gwammaja yace dole fa Gwamna Ganduje ya cire jar hula tun da yanzu ya baude. Alhaji Sharu Gwammaja yace sun ba Gwamnan awannin 48 da ya cire hular ko su shiga Kotu


‘Yan Kwankwasiyya  sun ce Ganduje nacin alfarmar jar hula wajen mutanen Kano, duk cewa ba dan ta bane. ‘Yan Kwankwasiyya sun ba mutanen Kano hakuri da suka tsaida masu Ganduje a matsayin Gwamna, suka ce ai an kuma gama. 



A Karanta sauran manyan labarai na Kasa a shafin NAIJ Hausa

@Ya_waliyyi

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...