Sunday, October 30, 2016

Shugaba Buhari yayi magana game da Mamman Daura



Alhaji Mamman wa? 




Anyi wata hira da Shugaba Buhari inda aka tambaye sa ko da gaske ba shine ke rike da madafan ikon Gwamnatin nasa ba

 



Shugaba Buhari yace shi kadai ya nemi takara, kuma shi yayi yawon neman kuri’a don haka shine kadai Shugaban Kasa

 



Shugaban Kasar yace wadanda su ke ganin ba a tafi da su ba, can da su gada



Shugaba Buhari yayi wata hira inda aka yi masa wata tambaya game da rade-radin da ake yin a cewa akwai wani Alhaji Mamman Daura wanda shine kamar Shugaban Kasar. Shugaba Buhari yace wannan karya ce ake yi musamman daga Gidan labarai na Sahara Reporters, yace bai san inda suke samo labaran su ba.

Shugaba Buhari yace shi kadai ya nemi takarar Shugabancin Kasar nan, lungu da sako na Najeriya, a jirgi da mota, don haka shi kadai ne Shugaban Kasa ba wani ba. Shugaba Buhari ya kara tambayar ‘Yar Jarida ko shin Mamman wa take nufi da ta kira sunan Alhaji Mamman Daura da ake zargin ya rike madafan ikon Kasar. Yace wannan karyar banza ce.

Shugaba Buhari yace bai yadda da ballewar Biafra daga Kasar ba, sai dai ya kira su da su shigo Jam’iyya a buga siyasa da su. Shugaba Buhari kuma ya bayyana shirin taimakon Yankin da Boko Haram suka yi wa barna.

Shugaban Kasar ya kuma ce a karshe duk wanda yake ganin an ware sa a Gwamnati, wannan matsalar su ce, don kuwa shi bai da wata matsala.

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...