Muhammadu Buhari ya aika da takardar kasafin kudin shekara mai zuwa
Reuters ta rahoto cewa har Shugaban Kasar Najeriya
Muhammadu Buhari ya fara aikawa
da takardun kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2017 zuwa Majalisar Dattawa ta
Kasar. Shugaban
Kasa
Muhammadu Buhari ya mika
takardar da za a duba kasafin kudin shekara mai zuwan ne domin a amince.
Wannan takarda tana dauke da
yadda Najeriya za ta kashe kudin ta shekara mai zuwa, har sai Majalisar
dattawar Kasar ta amince sannan za a kawo ainihin kundin kasafin kudin shekara
mai zuwan ta 2017.
KU KARANTA: Shugaba Buhari ya aika da kasafin kudi
Majalisa
Takardar ta nuna cewa
Najeriya za ta kashe Fiye da Tiriliyan shida da biliyan dari takwas, 6.86tr
watau dala biliyan $22.57 a shekara mai zuwa. Wannan kudi dai ya ma fi na bana
da aka lissafa Tiriliyan 6.06. Najeriya dai ba ta taba kasafin irin wannan
makudan kudin ba a Tarihi.
Tattalin arziki Najeriya dai
ya ruguje bayan karyewar darajar mai a duniya, haka kuma Kasar ba fama da
Tsagerun Neja-Delta wanda suke fasa butatan man Kasar, don haka gangan man da
Kasar ta ke fitarwa sun ragu sosai. An dai kiyasta gangar mai a kan $42.5 a
kasafin na 2017, da kuma $1 a kan N300.2500.
Ga shi ma dai kuma Hon. Jibrin ba ya nan.
Muhammad Malumfashi ya rubuta wannan rahoto a shafin NAIJ.com:
Domin karanta wasu labaran sai a garzaya shafi na na NAIJ Hausa: https://www.naij.com/author/muhammad-malumfashi.html
Twitter: @ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment