Allah yayi an gano Zainab Sultaana a hannun wasu mutane
– A Jihar Kaduna an gano wata yarinya bayan watanni bakwai da bacewar ta hannun wasu mutane
– An sace Zainab Sultana Umar ne a lokacin da ta bar gida zuwa Islamiya a farkon shekarar nan
– Yanzu haka an kama wadanda suka dauke ta, har suka ce diyar su ce
Wani abin mamaki ya faru a
Unguwar Badikko ta Jihar Kaduna, an gano wata yarinya da aka cire tsammanin ta
hannun wasu mutane. An sace wannan ‘Yar karamar yarinya mai shekaru kimanin
biyar ne a Jajere road da ke Unguwar Badiko a watan Maris za ta je Makarantar
Islamiyya.
An sace wannan yarinya mai
suna Zainab da ake kira Sultana ne a watan Maris din shekarar nan, har dai
iyayen ta sun cire rai. Asali ma tuni suka maidawa yarinyar da suka haifa sunan
wanda ta bace. Sai ga shi kwatsam wani danuwan ta mai suna Malam Umar ya gan ta
wajen wata mata Inyamura a garin. Yana kuwa kiran sunan ta, ta amsa. Sai dai
wadanda suka sace tan, sun yi karfin halin cewa diyar su ce, su suka haife ta.
Tuni dai Jami’an tsaro suka
shiga binciken lamarin, aka wuce da mutanen wajen Hukuma. Mai girma Gwamnan
Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai ya leka wajen da abin ya faru. ‘Yar yarinyar
da aka sace Zainab watau Sultana har ta zama ba ta jin Hausa sai dai irin su
yaren Ibo. Wata majiyar ta ce da kyar ma gane iyayen ta, watakila anyi mata
asari ne.
Jami’an ‘Yan sanda dai sun
kama wannan mutumi da ya sace ta, kuma ana zargin cewa mutumin Adamawa ne,
matar sa kuma ana tunani Inyamura ce. A wani faifan bidiyo da ya zo mana,
wannan mutumi ya fadawa Jami’an ‘Yan sanda cewa shi ba sa da wani mugun nufi.
Ya ma sa ta a makaranta, ya kuma yi mata fasfo na Kasar waje. Ko da ma can yace
shi dan kasuwa ne a Dubai. Wasu dai suna cewa sufarar yara yake yi. Yace shi
yana sha’awar diya mace, shiyasa da ya gan ta a lokacin, sai yace mata, ta zo,
hakan kuwa aka yi.
Muhammad Malumfashi ya rahoto wannan labari daga Garin Kaduna
Twitter: @Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment