Saturday, October 22, 2016

Najeriya da Tattalin Arziki, A. Mati

NAJERIYA TA DAWO TA DAYA A TATTALIN A ARZIKI AFRIKA





Kula da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin Najeriya take yi, kwatsam sai ga hukumar bada lamuni ta Kasa wato IMF ta fito ta ce Tattalin Arzikin Najeriya shine mafi girma a nahiyar Afrika, amma abin ban al’ajabin shine, wata biyu baya wannan dai hukumar tace tattalin arzikin Najeriya ya koma  na biyu a Afrika wato bayan kasar Afrika Ta Kudu, ba shakka wannan rahoton ya jawo kace-nace a Najeriya, shiyasa babban dan kasuwar nan na Najeriya wato Aliko Dangote ya fito yace shi fa sam bai yadda cewa tattalin arzikin Najeriya ya koma na biyu a Afrika ba, yace idan ka lura da girman kasar da irin kudaden da ake juyawa, yace zai wuya ace wai wata kasa ta wuce Najeriya a girman tattalin arziki a nahiyar Afrika. Toh masana dai suna ta bayanin abinda ya jawo hakar, wato yadda cikin kankanin lokaci ita hukumar bada lamunin tai amai ta lashe, turkashi, jama’a dai sunata tofa albarkacin bakin su, wasu suna ganin cewa da gangan ita hukumar tai hakan don su ciwa Najeriya mutunci a idon duniya, wasu kuma suna ganin cewa inaa, ai ita hukumar tana anfani ne da bayanai da alkaluma da take da shi kan Kasashe wajen fitar da irin wannan bayanan, saboda haka bakada hujjar da zaka zargesu da yin ba daidai ba.

Ita Hukumar Bada Lamunin tace bayan an kara lissafi akan alkalumar tattalin arziki wadda ya fito a watar Agusta ya nuna cewa Tattalin Arzikin kasar Afrika ta Kudu nada nauyin Dalar Amurka biliyan dari uku da daya, ita kuma Najeriya tana da dalar Amurka biliyan dari biyu da casa’in da shidda (idan aka kula da darajar musayar kudi) wannan rahotan ya fito ne a watar agusta na wannan shekarar.
Amma kuma sabon kintace da Hukumar Bada Lamunin ta kara yi, ya nuna cewa tattalin arzikin Najeriya fa yayi yunkuri ya dawo na daya a Nahiyar Afrika wato gaba da kasar Afrika ta Kudu da Kasar Algeria. Suka ce arzikin Najeriya ta hau zuwa dalar amurka biliyan dari hudu da sha biyar da digo takwas. Ita kuma Afrika ta Kudu dala biliyan dari biyu da tamanin da digo uku na kudin amurka, itama kasar Algeria dalar amurka biliyan dari daya da sittin da takwas da digo uku. Duk da cewa ita hukumar kula da bada lamuni ta kasa wato IMF ta nuna cewa tattalin arziki na duniya gaba daya yana fuskantar barazana na rashin cigaba na azo a gani.

Ita ma hukumar da take auna ingancin tattalin arzikin kasa ta FITCH Ratings tace Tattalin Arzikin Najeriya zata samu walwala a shekara ta 2017, domin tace tattalin arzikin Najeriya zai girma da kashi biyu da digo shidda 2.6% bayan halin kunci da ta samu kanta a shekara ta dubu biyu da shashidda 2016 da kashi daya da digo biyar wato 1.5%. ita dai wannan hukumar tayi bayani cewa tsarin darajar musayar kudi da babban bankin Najeriya ta kawo ta taimaka wajen canjin alkalumar sannan kuma kudinda ake sa ran Gwamnatin Tarayya ta kasha wajen manyan ayyuka a kasar idan ya yiyu zai matukar taimakawa wajen gyara tattalin arzikin kasan Najeriya.

Duk da abinda wannan cibiyoyin  suka ce, wasu dai ‘yan Najeriya sunce fa wannan cangin alkalumar ba zai rasa nasaba da gagarumar noman da akayi wannan shekarar ba, wanda masu lura sukace an dauki shekaru masu yawa robon da ai irin wannan noman na ba kama hannun yaro. Kuma da haka ne masu lura da tattalin arziki suke cewa lallai fa ‘yan Najeriya sai sun kara hakuri sosai sun maida hankali kan noma da kayayyakin da ake kera su a Najeriya, cewa hakan shine fa zai ceto kasar daga cikin halin da take ciki na rashin aikin yi da rashin samun kudin shiga ga gwamnati.        

Ahmad Mati ya rubuta wannan
Yana shafin Twitter: @ahmadmati1

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...