Monday, October 17, 2016

Sheikh Sani Rijiyar-Lemu ya gargadi Sanatocin Najeriya



Sheikh Muhammad Sani Umar  Rijiyar-Lemu



Kudirin daidaita Rabon Gado: Sheikh Umar Sani Rijiyar-Lemu ya ja kunnen Sanatocin Najeriya


– Wani Babban Malami a Kasar nan ya ja kunnen Sanatocin Najeriya game da kudirin rabon gado

Dr. Muhammad Sani Rijiyar-Lemu ya gargadi Sanatoci game da yunkurin raba kason gadon maza daidai da mata



Malamin yace wannan ya sabawa addinin musulunci kuma tsokanar fada ce

 

 

Wani Babban Malamin Musulunci Sheikh Muhammad Sani Umar Rijiyar-Lemu ya gargadi Sanatocin Najeriya game da yunkurin kawo wata doka da za ta sa rabon gadon namiji ya zama daidai da na diya mace a Kasar nan. Wata Sanata mai suna Abiodun Olujimi daga Ekiti ta kawo wannan kudiri.

 Sanata Misis Biodun Olujimi ta kawo kudirin daidaita kason namiji da mace a Majalisa

Babban malamin da ke Kano yace wannan doka ta sabawa Addinin musulunci, Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar-Lemu yace akwai yi wa Addinin Musulunci Karen-tsaye da kuma tsogala a wannan kudiri. 

Malamin yace akwai yadda shari’a ta tsara rabon gado a addini cikin Hikima kuma babu yadda za ayi a canza wannan. Asali ma duk musulmin da ya musanya hakan, yayi ridda daga musulunci, don kuwa yayi fito-na-fito da Shari'ar Allah. Dakta Rijiyar-Lemu ya kira Sanatocin Najeriya musamman wanda suke Musulami da ke Majalisar da su guji amincewa da wannan kudiri. 

Tun a ranar farko dai wani Sanata Kirista mai suna Emmanuel Bwacha yace hakan ya saba addinin Kiristanci, inda ya janyo nassoshi daga Littafin sa.
 
A baya wani Shehin Malami a Kasar nan , Dahiru Bauchi yayi kira ga Sanatocin Kasar da su bi a sannu game da abubuwan da suka shafi addini a Kasar. Sheikh Dahiru Bauchi yace musulunci ya tsara ka’idar rabon gado a Kur’ani. 

Haka ma Kungiyar Izala watau JIBWIS karkashin Sheikh Yusuf Sambo Rigachikun ma dai tace wannan kudiri ya sabawa shari'ar Musulunci. 

A musulunci dai namiji na karbar kashi biyun na mace a wasu yanayin, saboda kuwa a ko yaushe, da namiji shi yake kula da mace. 


Muhammad Malumfashi daga Zariya
@Ya_waliyyi

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...