Shugaba
Buhari: Damukaradiyya da Mulkin Soja
Shugaba Muhammadu Buhari ya
mulki Kasar nan a lokacin Soji daga Disamban 1983 zuwa Agustan shekarar 1985. A
ranar 29 ga watan Mayun bara kuwa ya kara darewa mulkin Kasar, a matsayin
Shugaba na 15 a Najeriya, sai dai a wannan karo, mulkin farar hula. Wanda hakan
ta sa ya zama mutum na farko bayan Obasanjo da ya mulki Kasar sau biyu; a karo
na Soji da Damukaradiyya.
Sanannen abu ne cewa Shugaba
Buhari ya dade yana neman takarar Shugabancin Kasar nan, har yayi ya gaji. Har
sai shekarar 2015, inda ya samu sa’ar buge Tsohon Shugaba Jonathan Goodluck.
Mutane da dama dai ba su yi amanna da Buhari ba saboda suna ganin cewa, Soja
kowa ya tube kaya, yana gida, Soja ne. Duk da cewa ya sha jaddada riddar sa
gaban duniya, ya zama dan siyasa na damukaradiyya; tun bayan kifewar Daular
Tarayyar Kasar Russia. Wasu dai suna ganin anya wannan Janar din zai fasa halin
sa-na Soja idan ya samu mulki?
Duk da cewa wani zai iya ce
maka ai tuwo ba ya taba canza suna. Ko a yanzu a mulkin Shugaba Buhari an zarge
sa da karya hakkin bil adama, kamar yadda ya kama Sambo Dasuki, Nnamdi Kanu da
Ibrahim Zakzaky ya garkame. Ga shi ya rufe hanyoyin shiga na ‘border’ kamar
yadda dai yayi a baya, ga wani tsarin kasuwanci da yake kokarin kullawa da Kasar China, dsr dai. Ga kuma
yunwar Buhariyyah, ta dawo…Sai dai mun kawo maku irin bambancin da aka samu
tsakanin zuwan Shugaba Buharin na farko da kuma na yanzu:
Cire tallafin man fetur
‘Subsidy’
Babu irin matsin da Shugaba
Buhari bai sha ba a shekarun 84-85 na ya cire tallafin man fetur, da na sauran
kayayyaki; Sai dai Janar din ya hau kujerar na-ki, yace sam ba zai yi hakan ba,
don talakawa. Sai ga shi abin mamaki, wannan karon ya cire tallafin man fetur
din. Ko a zamanin Shugaba Jonathan, Buhari bai amince da cire tallafin ba.
Wannan karan kuwa, dara ta ci gida, sai dai ‘Yan Najeriya ba su yi masa bore
ba. A baya dai Najeriya ta saba biyan kudi da ya kan wuce Naira Tiriliyan guda
kan tallafi, mafi yawa kuma ana tunanin aljihun bogi yake zarcewa. Yanzu dai
man fetur din da Najeriya ta ke sha ya ragu, da alamar tambaya.
Karya farashin dala
‘Devaluation’
Haka dai a wancan lokaci,
cikin sharuddan da Kungiyar IMF ta ba sa, akwai karya farashin kudin Naira, nan
ma Janar Buhari yace ‘Ina’ Kamar dai batun ‘Subsidy’, Bankin CBN na Kasar ya
saki farashin kudin Nairar a sama yana lilo-inda kasuwa ta kada da shi, ba dai
kamar yadda Shugaba Buhari ya so ba. Farkon hawan mulkin sa, yayi kokarin
tokare darajar Nairar da ‘Yan dalar da Kasar ta ke da su, sai dai aikin ya wuce
nan.
Majalisa
Aiki da Majalisa bakon abu
ne wajen Shugaba Janar Buhari, ya kuwa yayi iya bakin gwargwado. Tun fari,
Shugaba Buhari yace ba zai tsoma baki cikin sha’anin zabenMajalisun Kasar ba,
yin hakan dai ya zo da irin na sa cikas din. Ba kamar yadda yayi a baya ba, sai
dai kawai Fadar Koli ko na Tarayya na Soji ‘Supreme Military Council’ da
‘Federal Military Council’ ta murza gashin baki, tace ga yadda za ayi. Asali ma
dai Shugaban na da kudurori da dama gaban Majalisar, tun bara wanda sun ki cewa
ko ‘hmm’, wasu kuma na tafe, ko ya za a kaya? Ko dai fita Kasar waje Shugaban
Kasar zai yi, sai ya rubutawa Majalisar takarda. Ga batun kasafin kudi da aka
yi ta fadi-tashi.
Neman hana ‘yan jarida
Magana
A shekarar 1984, Shugaba
Buhari ya kirkiro wata Doka mai lamba 4, wanda tace duk dan jaridar da ya
rubuta karya game da Gwamnati, zai sha dauri ko tara na kudi. Hakan ta sa aka
daure wasu ‘yan jarida a Kasar, a bara wani Sanatan majalisar Dattawa na Kasar
nan, ya nemi ya kawo irin wannan kudiri a Majalisa, sai dai tuni Shugaba Buhari
yace wannan ba da shi ba.
Ministoci
Dole wannan karo Shugaba
Buhari ya bi kundin tsarin mulkin Kasa wajen nada Ministoci, bayan dogon
lokaci, ya nada Ministoci; guda daya daga kowace Jiha. Ba kuwa haka aka saba a
mulkin Soji ba, ka iya ganin wata Jiha ba ta da wakili a Majalisar zartarwar.
Sai dai Buhari ya nada kan sa a matsayin Ministan man fetur, ko can dai ya rike
irin wannan matsayi a baya kafin ya zama Shugaban Kasa.
Matar Shugaban Kasa
A wancan karo ba a san Matar
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ba sosai-Hajiya Safinatu. A bara kuwa wajen
yakin neman zabe, ‘Yan Najeriya sun ga Aisha Buhari-Matar Muhammadu Buhari. Ta
kuwa yi alkawari kamar na mai gidan ta, cewa ba za ta kama Ofis ba na
‘Uwargidan Najeriya’ kamar yadda aka saba don ya saba dokar Kasa. Sai ga shi
yanzu ta kan je har Amurka, har da mai mata kwaliyya, amma a matsayin ‘Wife of
the President’ ba kuwa ‘First lady’ ba, watau Matar Shugaban Kasa, ba Uwargidan
sa ba. To ai an ki cin biri, an ci dila.
Kasafin Kudi da Ayyukan Kasa…
Bayan hanbarar da Gwamnatin
Shehu Shagari, Buhari ya rage kasafin kudin Kasar na shekarar da ta biyo, sai
dai wannan karo, Shugaba Buhari ya ma kara karfin kasafin Kudin Kasar Najeriya
ne a wannan shekarar, daga Tiriliyan hudu da rabi zuwa fiye da Tiriliyan shida.
Kamar dai yadda ya kara
karfin kasafin kudin Kasar nan, Shugaba Buhari ya kara yawan kudin da aka ware
na ayyuka-irin su tituna, gada, gidaje dsr. Shugaban Kasar ya ware kusan rabin
Tiriliyan wajen wannan, ba ma za a hada da abin da Gwamnatocin baya suka saba
ba. A shekarun Soji kuwa, Buhari tsaida duk wasu manyan ayyuka da Shagari ya
fara, da cewar babu kudi. Haka kuma akwai shirin daukar ma’aikata da dama har
sama da 500000, a mulkin Soji kuwa, Janar Buhari yayi sanadiyyar rasa aikin
mutane dubunnai.
Bindige ‘yan kwaya
A lokacin Soji, Janar Buhari
ya harbe wadanda aka kama da laifin safarar kwayoyi har lahira, mace da namiji,
babba da yaro. A wani kaulin, wannan na daga cikn dalilin da ya sa aka kifar da
Gwamnatin sa. Sai dai wannan karo babu wata doka mai kama da wancan mai lamba
ta 20. Amma dai, ‘Yan Kwastam da Ma’aikatan hanyoyin ruwa sun rufe shigo da
kayan jabu.
Rancen kudi wajen Gwamnatin
Jihohi
A lokacin mulkin Soji,
Buhari ya haramtawa masu rike da Jihohin Kasar cin bashi ko ta wani iri. Kamar
dai yadda ya karbi (ko ace ya kwata) mulkin Kasar daga hannun Shagari,
Gwamnoni da dama sun gaza biyan albashin Ma’ikatan su, a mulkin Tsohon Shugaba
Jonathan. Gwamnatin Buhari ta bada aron kudi domin a biya ma’aikatan Jihohi,
kwanan nan ma kum, Gwamantin Tarayya ta kara fito da wani sabon tsarin rancen
ga Gwamnatin Jihohin Kasar.
Yaki da Cin Hanci da Rashawa
Har yanzu dai babban dodon da Shugaba Buhari yake fada da
shi, shi ne Rashawa a Najeriya. Ko da dai bai sauka daga wannan matsayin ba,
sai dai salon ya canza. A zamanin Soji, ya kama ‘yan siyasa da dama ya daure,
sai dai kowa tashi ta fishe shi. Yanzu kuwa, tsarin mulkin Kasa yace barawon da ba a kama ba, sunan sa Muhammadu
ba kamar da can da Buhari ya rika amfani da tsarin ‘Na shiga ban dauka ba... ba ta fitar da barawo’ ba. Da bakin sa
yace yanzu sai ya ga wadanda suka shiga Gwamnati a cikin manyan motoci, amma
tsarin mulki yace har sai an kama su da laifi baro-baro. Ba don haka ba da tuni
an maimaita na Ummaru Dikko da Deziani Madukwe.
No comments:
Post a Comment