– A Jihar Delta Wata Amarya ta ruga a guje yayin da ske shirin daura mata aure
– Wannan Amarya ta ce ba tayi, ana tsakiyar taro
– An ga Angon ta a guje yana bin ta a baya, yana ba ta hakuri
A Jihar Delta wani abin
mamaki da al’aji ya faru a wannan makon. DailyPost ta rahoto cewa an dakatar da
wani daurin aure bayan da Amarya ta sheka a guje ta bar wurin bikin. Wannan
Amarya ta ce ita fa sam ta fasa yin auren.
Bayan ta ruga, can aka hangi
Angon ta a baya yana gudu, domin ya shawo kan ta, ya ba ta hakuri. Wannan abu
dai ya faru ne a Garin Udu da ke Jihar Delta. Mutane ne dai sun tsaya kallon
sarautar Ubangiji, inda suka ga Ango ya bi kan titin Orhunworhun a guje yana neman Amarya ta dawo a daura masu aure.
Ana dai cikin tsakiyar biki,
wannan Amarya ta arce a guje ta bar dakin taron, tace fau-fau ta kuma fasa
auren. Sai dai har yanzu ba a san menene ya faru, ya jawo hakan ba. Amma dai
wannan abu ya ba jama’a mamaki kwarai.
No comments:
Post a Comment