Monday, October 31, 2016

Na fasa: Amarya ta tsere ana tsakiyar daura aure...


– A Jihar Delta Wata Amarya ta ruga a guje yayin da ske shirin daura mata aure

 


Wannan Amarya ta ce ba tayi, ana tsakiyar taro

 


An ga Angon ta a guje yana bin ta a baya, yana ba ta hakuri





A Jihar Delta wani abin mamaki da al’aji ya faru a wannan makon. DailyPost ta rahoto cewa an dakatar da wani daurin aure bayan da Amarya ta sheka a guje ta bar wurin bikin. Wannan Amarya ta ce ita fa sam ta fasa yin auren. 

Bayan ta ruga, can aka hangi Angon ta a baya yana gudu, domin ya shawo kan ta, ya ba ta hakuri. Wannan abu dai ya faru ne a Garin Udu da ke Jihar Delta. Mutane ne dai sun tsaya kallon sarautar Ubangiji, inda suka ga Ango ya bi kan titin Orhunworhun a guje yana neman Amarya ta dawo a daura masu aure.

Ana dai cikin tsakiyar biki, wannan Amarya ta arce a guje ta bar dakin taron, tace fau-fau ta kuma fasa auren. Sai dai har yanzu ba a san menene ya faru, ya jawo hakan ba. Amma dai wannan abu ya ba jama’a mamaki kwarai.


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...