– Bello Abubakar Masaba, mutumin da yake da mata barkatai yace fa yana nan lafiya lau, bai mutu ba
– Masaba yana da mata fiye da 80
– A ranar Asabar aka yi ta yada labarin cewa Bello Masaba ya rasu, yace ko rashin lafiya bai yi ba
Idan ba a manta Bello
Abubakar Masaba, wani mutumin Bida ta Jihar Neja mai mata barkatai. A karshen
makon nan ne aka yi ta yada rade-radin cewa ya mutu a Ranar Asabar din nan, aka
ce wai yayi ta rashin lafiya, yayi jinya.
Sai kuwa ga shi Bello Masaba
ya fito yace yana nan fa da ran sa, ya bayyana haka ne ta wayar tarho da yayi
da ‘Yan jaridar Daily Trust. Masaba yace ko kwarzane bai yi ba, balle wani
ciwo, ina kuma ga mutuwa? Yace yana nan cikin koshin lafiya da ran sa.
Masaba yace makiya ne kurum
ke yada karyar mutuwar sa, sai dai yace Ubangiji ya fi su, ya kuma sa ya sha
gaban su. Bello Masaba yace ‘ku zo Bida, za ku same ni, da iyali na cikin
koshin lafiya…’ Masaba yace wasu marasa imani ne kurum suka yada wannan karya.
Bello Masaba dai kowa ya san
sa da tarin mata, mai mata 86, yayi mata kusan guda 107, har yanzu kuma
yana tare da kusan guda 80, bayan ya rabu da wasu da dama. Yana da ‘ya ‘ya guda
185, sai dai wasu daya sun rasu, yanzy ‘ya ‘yan na sa ba su wuce guda 133.

Twitter: @Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment