Rayuwa
kenan: Jama’a sun taru wajen rufe Marigayi Dan Masanin Kano
- Gwamnan Kano ya jagoranci jama’a wajen birne
Marigayi Maitama Sule
- Shugaban Majalisa Bukola Saraki yana cikin
wadanda suka halarci sallar
- Sauran manyan Gwamnoni da mutanen Kasa sun yi
Dattijon Sallah
A jiya ne Dan Masanin Kano ya cika a wani Asibitin kasar
Masar. Manyan Kasa dai sun halarci sallar da aka yi masa. Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Ganduje ya
jagoranci jama’a wajen birne tsohon Ministan.
Sauran Gwamnonin Jihohin Jigawa, Bauchi da Sokoto, dsr sun
halarci sallar. Haka kuma Shugaban Majalisar Dattawa Dr. Bukola Saraki yana
cikin wadanda suka halarci sallar. Sauran Ministocin kasar irin su Hadi Sirika
da Kayode Fayemi sun halarci Jana’izar.
Gwamnatin Tarayya ta aiko wakilai karkashin Shugaban
Ma’aikatan gidan Gwamnati Abba Kyari. A jiya Shugaba Buhari
ya aiko takarda ta musamman inda yake takaicin rashin Maitama Yusuf yace an yi
rashi.
Babban Jigo a Jam’iyyar
APC Bola Tinubu yace ba shakka an rasa wadanda su ka rage cikin iyayen kasar da
ake da su. Dan Masanin Kano mutum
ne mai baiwar magana kuma mai son kasar nan da gaskiya.
[NAIJ Hausa]
Allah Ya gafarta masa, mu kuma Allah Ya Sa mu cika da kyau da imani.
ReplyDelete