Kasar Koriya ta Arewa ta kara harba wani mugun makami mai linzami
- Kasar Koriya ta Arewa ta yi gaba
wajen harkar nukiliya
- Kwanan nan Kasar ta kara harba
wani makamin
- Wannan ne karo na biyu da kasar
ta harba nukiliya
Mun
samu labari cewa Kasar Koriya ta Arewa ta yi gaba wajen harkar nukiliya don
kuwa Kwanan nan Kasar ta kara sakin wani mugun makamin.
Ku
na sane cewa wannan ne karo na biyu da kasar ta harba nukiliya cikin 'yan
kwanakin nan domin wani gwajin da ta ke yi. Makamin wannan karon ma dai ya fi
wanda aka saki a baya. Kwanaki kasar ta saki irin wannan makami da zai iya
barin Nahiya zuwa wata Nahiyar.
BBC
ta rahoto cewa wannan makami ya dade yana yawo kafin ya fada cikin ruwa a wani
Gari cikin Kasar Japan. Duk da dai takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta ke
dorawa Kasar ta Koriya ta Kudu ba ta tsaya wajen harkar kera makamin ba.
Kwankin
baya Kasar Koriya ta Arewa ta saki wani mugun makami mai linzami wanda ka iya
dura kan Garin Alaska. Amurka tace dole a takawa Koriya burki ko ta karfi da
yaji idan ta kama don ta saba doka bayan da ta saki wani mahaukacin makami mai
linzami.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment