Wani mutumi yayi da'awar Annabta a Kasar Sudan
- Wani mutumi yace shi Annabi ne kuma
ana yi masa wahayi
- Wannan mutumi ya fito ne daga
Yankin Darfur ta kasar Sudan
- Har da ma wata sura yace an sauke
masa ga mutanen sa
Wani
mutumi mai suna Abdulwahid Muhammad Nur a can kasar Sudan yace wai shi ma Annabin
Allah ne kuma Ubangiji ya turo sa ga mutanen sa.
Wannan
'Dan banza yace ana yi masa wahayi kamar dai Annabawan Allah kuma tuni har an
sauko masa da wata Sura mai suna Sural Darfur watau ta mutanen Garin Darfur da
ke Kasar Sudan.
A
surar dai kamar yadda mu ka ji yana karanta ta, an ambaci mutanen Darfur da ma
na Nahiyar Afrika da kuma shi karen kan sa wannan mutumi a ayoyin ta.
Wannan mutumi Abdulwahid Muhammad yace Ubangiji ne ya aiko sa domin ya gargadi Jama'a daga azaba.
Wannan mutumi Abdulwahid Muhammad yace Ubangiji ne ya aiko sa domin ya gargadi Jama'a daga azaba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment