Sunday, July 23, 2017

Wani shu'umi a wata kasa yace shi ma Annabi ne



Wani mutumi yayi da'awar Annabta a Kasar Sudan



  • Wani mutumi yace shi Annabi ne kuma ana yi masa wahayi
  • Wannan mutumi ya fito ne daga Yankin Darfur ta kasar Sudan
  • Har da ma wata sura yace an sauke masa ga mutanen sa



Wani mutumi mai suna Abdulwahid Muhammad Nur a can kasar Sudan yace wai shi ma Annabin Allah ne kuma Ubangiji ya turo sa ga mutanen sa.

Wannan 'Dan banza yace ana yi masa wahayi kamar dai Annabawan Allah kuma tuni har an sauko masa da wata Sura mai suna Sural Darfur watau ta mutanen Garin Darfur da ke Kasar Sudan.

A surar dai kamar yadda mu ka ji yana karanta ta, an ambaci mutanen Darfur da ma na Nahiyar Afrika da kuma shi karen kan sa wannan mutumi a ayoyin ta. 

Wannan mutumi Abdulwahid Muhammad yace Ubangiji ne ya aiko sa domin ya gargadi Jama'a daga azaba.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...