Matar
Farfesa Osinbajo ta cika shekaru 50 a Duniya
- Matar Farfesa Yemi Osinbajo ta cika shekaru 50 a Duniya
- Mukaddashin Shugaban kasar ya taya ta murna cikin dare
- Farfesa Osinbajo yace yana alfahari da matar ta sa Dolapo
A safiyar yau ne Matar Farfesa
Yemi Osinbajo ta cika shekaru 50 a Duniya da haihuwa. Haka kuma Mijin na ta ya
dauki lokaci inda ya taya ta murnar zagayowar wannan rana.
Mukaddashin Shugaban
kasar Yemi Osinbajo ya taya Uwar ‘ya ‘yan ta sa 3 murna na musamman inda ya
kawo mata ‘dan kek cikin dare lokacin yayin da ba tayi tsammani ba. Osinbajo
yake cewa ita ce fika-fikan sa da yake tinkaho da su.
Shekaru fiye da 27
kenan da auren Farfesa Osinbajo da Dolapo wanda jika ce ta tsohon Firimiya na
Kasar Yarbawa Marigayi Cif Obafemi Awolowo. Matar Shugaban kasa watau Aisha
Buhari ta taya kawar ta murnar wannan rana.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment