Saturday, July 15, 2017

Abin sha’awa: Osinbajo ya taya matar sa murnar cika shekaru 50



Matar Farfesa Osinbajo ta cika shekaru 50 a Duniya 



  • Matar Farfesa Yemi Osinbajo ta cika shekaru 50 a Duniya
  • Mukaddashin Shugaban kasar ya taya ta murna cikin dare
  • Farfesa Osinbajo yace yana alfahari da matar ta sa Dolapo



A safiyar yau ne Matar Farfesa Yemi Osinbajo ta cika shekaru 50 a Duniya da haihuwa. Haka kuma Mijin na ta ya dauki lokaci inda ya taya ta murnar zagayowar wannan rana.

Mukaddashin Shugaban kasar Yemi Osinbajo ya taya Uwar ‘ya ‘yan ta sa 3 murna na musamman inda ya kawo mata ‘dan kek cikin dare lokacin yayin da ba tayi tsammani ba. Osinbajo yake cewa ita ce fika-fikan sa da yake tinkaho da su.

Shekaru fiye da 27 kenan da auren Farfesa Osinbajo da Dolapo wanda jika ce ta tsohon Firimiya na Kasar Yarbawa Marigayi Cif Obafemi Awolowo. Matar Shugaban kasa watau Aisha Buhari ta taya kawar ta murnar wannan rana.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...