Tuesday, July 18, 2017

Ashe akwai wanda ya fi Dangote kudi a Najeriya?




Ka ji Sanatan da ya fi Dangote arziki amma bai da ko gida a Abuja


  • Sanata Kabiru Marafa yayi da'awar kera Dangote dukiya
  • Sanatan yace a wajen sa wadatar zuciya ita ce Dukiya
  • Marafa yace idan kuwa haka ne to ya girmi Dangote a arziki





Sanata Kabiru Marafa na Jam'iyyar APC da ke Wakiltar Jihar Zamfara a Majalisar Dattawa yayi da'awar kera mai kudin Afrika Alhaji Aliko Dangote dukiya inda yace shi na shi mizanin awon dabam.

Babban Dan Majalisar yace a wajen sa shi wadatar zuciya ita ce arziki amma ba tsabar kudi ba. Sanatan yace idan kuma wannan ake magana to shi hamshakin attajiri ne don kuwa yana da wadatar zuci kwarai.

Sanatan yace har yanzu hayan gida yake yi a Abuja kuma yace kashi 60% cikin 100% na abin da ya samu hannun mutanen da su ka zabe sa yake komawa. Snatan dai ya nuna cewa bai da handama ko kadan.





[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...