An yi daurin gargajiyan Ahmed Musa
da Juliet a Garin Kuros Ribas
- An yi daurin gargajiyan Dan wasa Ahmed
Musa da Juliet
- Manyan ‘Yan wasan Najeriya sun
halarci wannan taro
- Daga ciki
akwai ‘Dan wasa Raheem Lawal na Super Eagles
Jiya ‘Yan
wasan Super Eagles suka isa Garin Kuros Riba. ‘Yan
kwallon sun je Garin ne domin daurin auren Ahmed Musa. Dan
wasan na Najeriya ya aure Sahibar sa Juliet a Garin su.
A
jiya 1 ga Wata ne aka yi daurin auren gargajiyan ‘Dan wasan gaban nan na Super Eagles
Ahmed Musa da kuma Sahibar sa Juliet Ejue a Garin Ogoja da ke Jihar asalin Kuros
Ribas inda matar ta sa ta fito. Idan ba a manta ba Mahaifiyar sa dai ‘Yar Jihar
Edo ce.
Manyan
‘Yan wasan Super Eagles irin su Raheem Lawal sun isa har kauyen Mbube domin
wannan babban taro. A baya dai an yi bikin auren wanda sai yanzu ne aka na
asalin gargajiyar. Ahmed Musa dai ya rabu da Matar sa Jamila kafin yayi wannan
aure.
A jiyan ne kuma babban Dan wasan Duniya Messi ya shiga
daga ciki. Lionel Messi ya auri sahibar sa mai suna Antonella Rocuzzo wanda su
ke tare su na yara.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment