Sunday, July 9, 2017

Yaki na nema ya barke tsakanin Amurka da Koriya ta Arewa


Yaki zai tashi tsakanin Kasar Amurka da Koriya ta Arewa?



  • Yaki na nema ya barke tsakanin Amurka da Kasar Koriya ta Arewa
  • Shugaban Amurka yace idan ta kama sai ya kai wa Koriya hari
  • Kwanan nan Koriya ta saki wani mugun makami mai linzami


Shugaban Kasar Amurka Donald Trump yace idan ta kama sai ya kai wa Koriya ta Arewa hari don ya taka masu burki wajen makami mai linzamin da su ke harbawa.

Kwanan nan Kasar Koriya ta Arewa ta saki wani mugun makami mai linzami wanda ka iya dura kan Garin Alaska. Amurka tace dole a takawa Koriya burki ko ta karfi da yaji idan ta kama don ta saba doka bayan da ta saki wani mahaukacin makami mai linzami.

Amurka tace za ta fi so a zauna yi sulhu amma fa idan abin ya faskara dole Kasar ta tashi tsaye. Kwanan nan dai Koriya ta saki makamin nukiliya da zai iya ratsawa har Kasar Amurka wanda Donald Trump yace ba zai yarda hakan ta faru ba.




[NAIJ Hausa] 

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...