Sunday, July 23, 2017

An yi wa El-Rufai kaca-kaca bayan ya soki su Sardauna


Mutane sun yi wa Gwamna El-Rufai kaca-kaca bayan ya soki su Sardauna


  • Mutane dai ba su ji dadin kalaman Gwamna El-Rufai ba
  • Nasir El-Rufai ya soki Marigayi Sardauna da su Zik
  • Tuni dai wasu su kace ba su cikin wannan magana





Mun fahimci cewa kalaman Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai bai yi wa jama'a dadi ba na sukar manyan kasar nan da yayi kwanan nan a wani bidiyo da ya bayyana. 

Gwamnan Malam Nasir El-Rufai yace su Sardauna sun yi sakaci wajen mulkin da suka yi. Yace Marigayi Sardauna Ahmadu Bello ba su yi kokari wajen gina kasar ba sai su ka buge da tada bangarorin su don manufar su ta siyasa.

Wasu dai sun ce wannan katobarar ba yau Gwamnan ya fara yin irin ta ba kuma ba su a cikin wannan suka. Wasu dai dama sun ce ai tun farko su Sardauna ba marasa yin laifi bane sai dai alherin su ya dara muguntar su.

El-rufai yace ko ba a fada ba manyan na wancan lokacin sun yi kuskure don kawai su ci ma burin su. Wani yace shi kan shi Gwamnan da bazar su yake rawa don haka ya ji da dai aikin gaban sa na Shugabancin Jihar Kaduna.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...