TAKAMA
DA MUSULUNCI
Hudubar Jumu’a daga Masallacin I.T.N Zangon-Shanu, Zaria
Daga Bakin Sheikh S.S Abubakar
Bayan shaidawa
da gaskiya cewa lallai babu abin bauta da gaskiya face Allah mai girma, shi
kadai yake bai da abokin Tarayya. Godiya da yabo sun tabbata a gare Sa, Shine
mai iko kan komai. Muna shaidawa cewa lallai Shugaban mu Annabi Muhammadu SAW
Bawan Allah ne kuma Manzon sa.
Bayan haka:
Duk wanda yake
da lafiyayyen hankali to yana da abin gadara a rayuwa. Amma fa babban abin gadara
shine addinin Musulunci wanda Allah ya yarda kuma ya zaba don shi ne mafificin
ni’ima da mutum zai samu a cikin rayuwar sa kamar yadda yake fada a Ranar da
aka kammala wannan addini. Allah SWT Yace ya cika n’ima a kan mu kuma ya zaba
mana Musulunci ya zama addinin mu. Saboda haka Musulmi na gaskiya a ko yaushe
yana takama ne da gadara da wannan ni’ima tare da aiki a lokutan sa ga wannan
addini.
Bayin Allah wannan
takama ba magana ce ta fatar baki ba, aiki ne tukuru in har mutum yana takama
da wannan addini. Sai mutum ya dage ya mike yayi aiki tukuru don cin burin
wannan addini na samun yardar Allah ta bin shiriyar Manzon Sa SAW a cikin
dukkan wani motsi a rayuwa.
Samun yardar
Allah Mai girma kan kasance ta hanyar kadaita Sa na dagewa da tsayawa kan
Tauhidi da bin hukuncin Allah da nisantar abin da Ya hana. A yayin yin hakan dole
mutum yayi kokarin tafiya tare da Iyalan sa ba wai shi kadai ba saboda wannan
maganar ceto ne daga wuta zuwa Rahama. Allah SWT yayi umarni a Qur’ani cewa Ku tseratar da kawunan ku da Iyalan ku daga
wuta wanda makamashin ta Mutane…Dole ne wannan ya ginu a bisa Imani da aiki
na kwarai. Allah Madakaki yana cewa Wadanda
su ka yi Imani da kuma aiki na gari za su samu Aljanna. Kuma dama Allah SWT
yace duk wanda aka tsirar daga wuta zuwa aljanna, hakika ya rabota! Manufar wannan
rayuwa dai ita ce bautawa Allah gwargwado kuma bissa yadda ya dace.
Babu wani dalili
na gadara da wannan Addini matukar ba ayi istikama kan shari’ar Allah ba. Kuma
wannan istikama ita ce bin tafarkin Allah mikakkiya kamar yadda duk Musulmi ke
roko a cikin kowace Sallah. A kan wannan dandamali da ke tsakanin umarni da
hani Musulmi na kwarai yake tafiya. Amma fa irin wannan tafarki na bukatar
abokan tafiya don haka sai Musulmi ya san irin abokan tafiyar na sa. Allah SWT ya
koyar da mu cewa mu nemi tafarkin da ba na wadanda aka yi fushi da su ko
batattu ba!
A yayin da ake
wannan tafiya kullum Musulmi dubawa zai yi ko su wanene abokan tafiyar sa kuma
dole su zama masu imani da Allah kuma wadanda su ka tsaya cak da bauta bisa
shiryar Manzo SAW tare da ado da halaye irin na Musulunci. A cikin wannan
tafiya ta neman dacewar Allah SWT to Musulmi ya san irin mutanen da zai tafi
tare da su. Mutanen na ba na kirki ba, sun san Mutanen su; Barawo ya san irin
mutanen sa idan har satar za ayi, haka ‘dan fashi da duk wani mai barna. Ta ya
mai imani da shiriya ya zama bai san Abokan tafiyar sa ba? Ya kamata Mai Imani
idan har ka gan sa tare da Mutanen banza to sai dai larura, kullum yana so ya
zama tare da masu gaskiya a matsayin majibinta. Allah yana cewa a Qur’ani mai
girma Muminai maza da Mata, sashen su na
tare da sashe. Haka kuma Kafirai su ma sashen
su na tare da sashe, har sai sun rasa na su, za su dauki Mumuni. Munafukai kuwa
Allah yace sashen su daga sashe yake gaba
daya. Haka wannan ya zo game da Azzalumai yayin da Allah SWT yake Gatan
masu Imani.
Jama’a kowa yana
takama ne da abokan tafiyar sa. A duk wani al’amari sai mutum ya nemi abokan
tafiyar san a kwarai; Daidai ga noma, Mutum kan nemi masu gaskiya ne da imani
irin sa a matsayin abokan tafiya, ba a zuwa a dauko maha’inta marasa gaskiya
wajen tafiya. Dukkan mai imani ya san abokan tafiyar sa. Saboda haka Bayin
Allah ku tsaya wajen tsare addini; ka da ayi rauni ko bakin ciki wajen wannan
jarrabawa.
Allah Madaukakin
Sarki game da mai takama da addini sa yace: ‘Wa ya fi kyawun magana irin wanda
yayi kira zuwa ga Allah yace kuma a tsaya a yi aiki na gari, a karshe kuma yace
ina cikin Musulmi!’ Babu wanda ya fi wanda yayi wannan kirari kyawun magana.
Jama’a ka da mu raina addinin mu wanda yayi mana tanadin rayuwa mai kyau a nan
Duniya da kuma Lahira. Idan mun shiga baki ciki sai mu koma mu duba inda mu
kayi sakaci wanda duk wannan amsa tana cikin addinin nan na mu. Lallai mu na
cikin gadara da wannan addini mai albarka kuma mu san abokan tafiyar mu sannan ka
da mu bari don rashin hangen nesa mu rungumi abokan tafiya na banza na daga kafirai
da sauran masu fasadi.
Allah ya bamu
ikon fahimtar AlKurani mai Girma da aiki da shi. Allah ya tserar da ni da k
duka daga azaba mai radadi ya shiga da mu Aljanna. Allah ka dada tsira ga
Annabi Muhammad SAW da iyalan sa da Halifofin sa, da sauran wadanda suka bi su
da kyautatawa. Allah ka taimaki Musulunci da Musulmai ka buwayar da Musulmai da
wannan addini na ka. Allah ka sa sahun Musulmi ya zama guda ka kuma raya wannan
kasa ta mu ka kare mu. Allah ka sa albarka bisa abubuwan da ka azurta mu da su.
Allah ka warkar da marasa lafiya musamman Shugaban wannan kasa ka kuma jikan
wadanda su ka rasu. Allah ka ba mu zama
lafiya kayi mana maganin Azzalumai da Fajirai ka tabbatar mana da alheri Duniya da Lahira.
-Mallam Salihu
S. Abubakar, Masallacin Islamic Trust of
Nigeria, ITN, Zaria.
Muhammad
Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Zaria
Twitter:
@Ya_waliyyi
No comments:
Post a Comment