Mutane
5 da su ka kai wa Shugaba Buhari ziyara a Landan
- Mun bi diddigi mun gano wasu daga cikin wadanda su ka iya ganawa da Buhari
- Tun bayan tafiyar Shugaban kasa Buhari babu wanda ya san halin da yake ciki
- Sai dai Matar sa da Mukadashin sa sun samu ganawa da shi a Birnin Landan
Mun bi diddigi daga
Jaridu irin su The Nation mun gano wasu ha kadan daga cikin wadanda su ka iya
ganawa da Shugaba Buhari tun bayan fitar sa Landan.
1.
Mukaddashin Shugaban kasa
Kun san cewa Mukaddashin
Shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya ma bayyana yadda su kayi da Shugaban
Kasa Muhammadu Buhari a Landan inda su ka hadu na fiye da awa guda a daren
Laraba.
2.
Uwargidan sa Aisha Buhari
Hajiya Aisha Buhari ta
kai ziyara Landan kusan ba sau daya ba ma inda ta gana da Mijin na ta kuma ta
kira ‘Ya Najeriya su cigaba da addu’a.
3.
Shugaban Hukumar DSS
Mallam Lawal Daura
wanda shi ne Shugaban Hukuar DSS da ke kula da kare Shugaban kasar ya samu
ganin Shugaban kasar.
4.
Ministan Ilmin Najeriya
Ministan Ilmi na kasa
Malam Adamu Adamu yana cikin wadanda su ka samu ganin Shugaba Buhari tun bayan
tafiyar sa. Alakar sa dai da Shugaba Buhari ba yau ta fara ba.
5.
Ministan Shari’a na kasa
Bayan Ministan Ilmi
Malam Adamu Adamu mun ji cewa Abubakar Malami wanda yake na hannun dama kuma
Ministan shari’a ya samu ganin Shugaban kasa Buhari kwanaki a Landan kafin haduwar sa da Osinbajo.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment