Sunday, July 16, 2017

Mutane 5 da su ka iya ganawa da Buhari a Landan


Mutane 5 da su ka kai wa Shugaba Buhari ziyara a Landan


  • Mun bi diddigi mun gano wasu daga cikin wadanda su ka iya ganawa da Buhari
  • Tun bayan tafiyar Shugaban kasa Buhari babu wanda ya san halin da yake ciki
  • Sai dai Matar sa da Mukadashin sa sun samu ganawa da shi a Birnin Landan


Mun bi diddigi daga Jaridu irin su The Nation mun gano wasu ha kadan daga cikin wadanda su ka iya ganawa da Shugaba Buhari tun bayan fitar sa Landan.


1.      Mukaddashin Shugaban kasa
Kun san cewa Mukaddashin Shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya ma bayyana yadda su kayi da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a Landan inda su ka hadu na fiye da awa guda a daren Laraba.

2.      Uwargidan sa Aisha Buhari
Hajiya Aisha Buhari ta kai ziyara Landan kusan ba sau daya ba ma inda ta gana da Mijin na ta kuma ta kira ‘Ya Najeriya su cigaba da addu’a.

3.      Shugaban Hukumar DSS
Mallam Lawal Daura wanda shi ne Shugaban Hukuar DSS da ke kula da kare Shugaban kasar ya samu ganin Shugaban kasar.

4.      Ministan Ilmin Najeriya
Ministan Ilmi na kasa Malam Adamu Adamu yana cikin wadanda su ka samu ganin Shugaba Buhari tun bayan tafiyar sa. Alakar sa dai da Shugaba Buhari ba yau ta fara ba.

5.      Ministan Shari’a na kasa
Bayan Ministan Ilmi Malam Adamu Adamu mun ji cewa Abubakar Malami wanda yake na hannun dama kuma Ministan shari’a ya samu ganin Shugaban kasa Buhari kwanaki a Landan kafin haduwar sa da Osinbajo.  



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...