Monday, July 3, 2017

Ashe kisan kare-dangi aka yi wa Fulani a Mambilla



Wata Shari'ar sai a Lahira: Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana abin da ya faru a Mambilla



  • Shugaban Gundumar Soji yace kusan da gan-gan aka kashe Fulani a Mambilla
  • Janar din yace da wuya ace babu hannun Hukuma da Jami’ai a barnar
  • Sojan yace wadanda su ka yi wannan aiki sun fi Boko Haram barna




Da laifin Shugabanni a rikicin Taraba-Sojin Najeriya

Shugaban Soji na Yankin Jos yace kisan kare dangi aka yi wa Fulani. Har mata masu ciki da kananan yara da shanu ba a bari ba. Bincike dai ya nuna cewa ba mamaki Hukuma na da laifi a ta’asar.

Bincike kamar yadda Shugaban Gundumar Sojin Najeriya na Runduna ta uku Birgediya Benjamin Ohanato ya nuna kusan kisan kare dangi aka yi wa Fulani a Garin Mambilla. Abin dai har mata masu ciki da kananan yara nmasu shekaru 2 da shanu ba a kyale ba.




Janar din yake cewa da wuya a yarda babu hannu ko sakacin Hukumar Jihar tun daga mataki na sama har kasa don ba ayi komai ba lokacin da barnar ta barke. Asali ma dai har lokacin da Soji su ka zo ana kona kauyukan Fulani. Sojan yayi tir da wannan yace har gara Boko Haram.

Kun ji cewa an kona gidaje da dama na Fulani a Mambila da ke Garin Sardauna. Mutane da yawa su ka rasa ran su inda wasu su ka samu rauni na inna-naha bayan sun tsere har ta kai wasu sun bar kasar zuwa Kamaru.




[NAIJ Hausa]

1 comment:

  1. Haqikah buri yayi kama da mutum! Gwamnati ya kamata ta dau tsautsaurar mataki tare da gudanar da cikakken bincike dangane da wagga al'amari.

    ReplyDelete

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...