Najeriya ta fara fitar da
doya zuwa Kasar China
- Yau Najeriya ta fara fitar da doya zuwa Kasar China
- Duk Duniya babu inda ya kai Najeriya noman rogo da doya
- Gwamnatin Shugaba Buhari ta dage
wajen harkar noma
Hakika
Shugaba Muhammadu Buhari ya dage wajen ganin an koma noma a kasar nan. Yanzu
haka Kasar Najeriya za ta fara fitar da doya a yau dinnan da mu ke magana. Tuni
kasashen China da sauran su suka nemi a kawo masu doya daga kasar nan.
Gwamnatin
Shugaba Muhammadu Buhari ta dage wajen harkar a kasar nan wanda yanzu har ta
kai yau za a fara fita da doya zuwa kasar waje. Ministan gona na kasar Cif Audu
Ogbeh ya tabbatar da wannan kamar yadda mu ka samu labari.
Kasar China watau Sin
dai tayi odar wannan kaya wanda zai ba Najeriya damar samun kudin kasar waje.
Duk Duniya babu inda ya kai Najeriya noman rogo da doya musamman ta bangaren
Arewa maso tsakiya na kasar.
A
bara an noma sama da ton miliyan biyu na shinkafa a Najeriya. Yanzu dai abin da
Najeriya ta ke fitarwa ya fi karfin abin da ake shigo da shi wanda shi ne
manufar Gwamnatin Shugaba Buhari.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment