Friday, June 9, 2017

Kasar Saudiya ta aikowa Najeriya goron azumi


Saudiya ta aikowa Najeriya ton 200 na kayan shan ruwa
 


– Saudi ta aikowa Najeeriya tumin dabino domin shan ruwa


Ofishin Jakadancin kasar ya tabbatar da wannan


– Ministar harkokin kasar waje ta godewa Saudiya da karamci



  • Za a rabawa ‘Yan gudun Hijira dabinon azumi
  • Saudi ce dai ta aikowa Najeriya ton 200 na dabino
  • Akwai dai alaka mai kyau tsakanin kasashen biyu


Ofishin Jakadancin Saudiya a Najeriya ta bakin Dr. Yahya Ali Mughram ya bayyana cewa kasar ta aikowa Najeriya ton 200 na dabino domin Musulmai su samu abin buda baki. Ana dai shiri tsakanin Najeriya da kasar mai tsarki.

An dai mikawa Ministar harkokin kasar waje Hajiya Khadija Bukar Abba wannan kayan alheri inda tayi godiya ga Kasar Saudiya ta kuma yi alkawarin raba kayan ga musamman ‘Yan gudun Hijira da ke Yankin Arewa maso gabas.

Kun ji cewa Sanatoci sun nemi rage kudin kujerar aikin Hajji na wannan shekarar kuma a daina karbar kudin abinci. Kudin kujerar aikin Hajjin bana dai ya haura Miliyan daya da rabi. Kwamitin harkokin kasar waje dai zai duba lamarin bayan kukan da Jama’a su kayi.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...