Sunday, June 25, 2017

An yi wa Shugaba Buhari addu’a a Sallar Idi


Hudubar Idi: Limamin ABU yayi kira ga ‘Yan Najeriya


  • Babban Limamin masallacin Jami’ar A.B.U yayi kira ga ‘Yan kasa
  • Sheikh Salihu Abubakar ya nemi ‘Yan Najeriya su daina dogaro da Gwamnati
  • Malamin yayi wa Kasar Najeriya da sauran Jama’a addu’a



Sheikh Salihu Abubakar ya kira Jama’a su tashi tsaye wajen kawo gyara. A cewar babban Shehin ba dole Gwamnati ce za tayi gyara ba. Malamin yayi wa kasa da Shugaba Buhari addu’a. 

Babban Limamin masallacin Jami’ar A.B.U watau Ahmadu Bello Sheikh Salihu Santalma Abubakar yayi kira ga ‘Yan Najeriya da su tashi tsaye kuma su daina dogara ko-ca-kam kan Gwamnatin Kasar. Haka kuma  Malamin yayi wa Shugaban kasa da Jama’a duk addua.


Babban Limamin masallacin Jami’ar A.B.U yayi kira ga ‘Yan kasa


Shehin Malamin yayi kira da ‘Yan kasa su dage a duk matakin da su ke na kawo gyara. Sheikh S.S Abubakar ya nemi Jama’a da su kawo gyara domin za a tambaye su duk inda su ka samu kan su domin kawo gyara na gari a cikin al’umma.

Kun ji cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aiko sakon Sallah ga ‘Yan Najeriya ta bakin mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai Mallam Garba Shehu. Shugaban Kasar yayi godiya inda ya kuma nemi a zauna lafiya a Najeriya.


           




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...