Gwamnatin Tarayya ta kauda zargi na yunkurin Musuluntar da Najeriya
- Gwamnatin Tarayya ta kauda duk wani zargi game da maganar wasu Fastoci
- Wasu na ganin akwai makarkashiya na tursasawa ‘Yan Najeriya Musulunci
- Gwamnatin kasar dai ta yi watsi da wannan maganar kamar yadda za ku ji
Wasu na ikirarin cewa
an soke ilmin addinin Kirista daga darussan Sakandare. Haka kuma ana yada cewa
an saka larabci da ilmin addinin musulunci. Ma’aikatar ilmi dai ta
wanke duk wannan zargi dalla-dalla.
Gwamnatin Tarayya ta
musanya zargin da ke yawo na cewa an soke ilmin addinin Kirista daga darussan makaruntun
Sakandare. Gaskiyar maganar dai ita ce tun lokacin tsohon Shugaba Jonathan aka
fara wani garambawul a tsarin ilmin kasar.
Yanzu haka dai an maida
darusan addinin musulunci da na kiristanci wuri guda inda kowane dalibi zai
dauki wanda ya dace karkashin wani darasi na dabam. Haka kuma an kawo yaren Larabci
tare da na Faransanci ga duk mai bukata amma babu dole a lamarin.
Bayan Kungiyar CAN ta Kiristoci, Fasto Johnson Solomon yace Gwamnatin Buhari na kokarin murkushe addinin Kiristanci a
kasar nan. Faston yace an soke ilmin addinin Kirista daga darasin makarantu
kuma aka bar na Arabi da Musulunci. Wannan magana dai ba daidai ba ce sam.
Idan ba ku manta ba a cikin kwanan nan ne aka kai
wani mugun hari a Garin Mambila da ke Jihar Taraba inda aka kashe Fulani da
dama bayan an kona gidajen su. Har yanzu Gwamnatin Jihar da ta Tarayya ba tayi
wa kowa jaje ko ta’aziyar Allah ya kyauta ba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment