Sunday, June 25, 2017

Sakon Shugaban Kasa Buhari na karamar Sallah




Sallar Idi: Sakon Shugaba Buhari ya kwantar da hankalin ‘Yan Najeriya

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aika sako ga mutanen Najeriya
  • Ana ma dai sa ran Shugaban kasar ya kusa dawowa Najeriya
  • Mun ji kishin-kishin din cewa dimuwa ta fara kama Shugaban kasar




Shugaba Buhari ya aiko sakon Sallah ga ‘Yan Najeriya ta bakin Garba Shehu. Shugaban Kasar yayi godiya inda ya nemi a zauna lafiya a Najeriya. Masu nazari kuma sun tabbatar da cewa muryar shugaban ce ba kage ba. Wannan dai ya sa hankalin da dama na kasar ya kwanta.

Yayin da wasu ke maganar cewa rashin lafiyar Shugaban kasa Muhammadu Buhari na kara tabarbarewa sai ga shi ya aiko sakon Sallah ga ‘Yan Najeriya inda yayi kira a cigaba da zama lafiya a kasa tare da addu’a domin sauke nauyin da ke kan Shugabannin.

Shugaban kasar dai ya godewa ‘Yan Najeriya game da irin addu’o’in da aka rika masa yayin da yake fama da jinya. Masu nazari dai sun ce ba shakka cewa muryar Shugaban kasar ce don kuwa ya taba abubuwan da su ke faruwa a kasa.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...