Friday, June 23, 2017

Najeriya za ta kere Amurka a wajen yawan Jama’a



Yawan mutanen Najeriya zai karu nan da 2050



  • Harsashe ya nuna cewa yawan mutanen Najeriya zai lula
  • A haka ma dai Najeriya ce ta 7 wajen yawa a Duniya
  • Zuwa shekarar 2050 kasar za ta kere Amurka
  • Kenan yawan 'Yan Najeriya zai zarce mutane Miliyan 300
  • Najeriya na da arziki amma 'Yan Najeriya na cikin talauci





Yawan mutanen Kasar Najeriya kara karuwa kurum yake yi. Nan da wani lokaci Najeriya za ta zama ta uku wajen adadin Jama’a. Kasar China da kuma India ne sahun gaba wajen yawan al’umma a Duniya. 

Wani harsashe da wata Hukuma da ke kula da yawan Jama’a na Duniya tayi ya nuna cewa Najeriya za ta kerewa Kasar Amurka wajen yawan mutane nan da shekarar 2050. Hakan na nufin Najeriya za ta zama ta uku wajen yawan Jama’a a kaf Duniya.






Zuwa wannan lokaci dai yawan haihuwar da ake samu a Nahiyar Afrika zai ribanya wanda ake samu a halin yanzu. Zuwa shekarar 2020 adadin Jama’an Duniya dai zai kusa Biliyan 10. Yanzu dai adadin mutanen Duniyar yak era mutum Biliyan 7.6.

Kasashe irin su Najeriya da China watau Sin, Indiya, Indonesiya, Fakistan da Amurka su na cikin wadanda su ka fi yawan al’umma a Duniya. Najeriya na fama da matsaloli daban-dabam irin na talauci, jahilci, kuncin rayuwa, yawan laifuffuka, ta'addanci da matsalar zamantakewa. 




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...