Friday, June 16, 2017

Falalar I’itikafi cikin karshen watan Azumi




Goron Azumi: Falalar I’itikafi a cikin watan Ramadan



  • Musulmai na azumi a fadin Duniya a cikin wannan wata
  • Akwai matukar lada ga wanda ya kebe a masallaci
  • Wannan kebewar ake kira I’itikafi a Addini



Akwai matukar lada ga wanda ya samu yin I’itikafi a cikin wannan wata. Manzon Allah SWT ya kan zauna a cikin masallaci yayi ta ibada. Ana so Musulmai su yi koyi da wannan ibada na Manzon Allah.

Yayin da ake azumin watan Ramadan yana daga cikin ayyukan lada shiga I’itikafi watau kebawa a Masallaci ba a wani aiki face salloli da karatun Al-kur’ani mai girma. A cikin Bukhari ya tabbata cewa Manzo SAW na yin I’itikafi a irin wannan lokaci na karshen Ramadan.

Akwai Hadisi daga Abdullahi ‘Dan gidan Abbas RA daga Manzo SAW da ke cewa duk wanda yayi I’itikafi a kwanaki goma na karshen Ramadan ba zai shiga wutar Jahannama ba. Wannan Hadisi dai Imam Tabarani ya kawo shi.




Ana shiga I’itikafi ne cikin watan Ramadan wanda aka fi ba karfi musamman a kwanaki goma na karshe. Sunnah ta tabbatar da cewa an fi so a shiga I’itikafi kafin rana ta fada kuma a fito da zarar an ce an ga wata watau kafin a shiga watan Eid.

Ana kuma I’itikafi ne a kowane Masallacin da ake Sallar Juma’a watau ba sai mutum ya fita domin zuwa Masallaci ba. Akwai dai Malamai irin su Nasir-Deen Albani da ke ganin Annabi SAW ya kayyade ga Masallatan nan uku mafi maraja.




[Muhammad Malumfashi ya fara rubuta wannan a NAIJ Hausa a matsayin goron Jumu'a]


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...