Thursday, June 8, 2017

Wani Gwamna ya shirya biki bayan Real Madrid ta ci kofi



UCL: Ka ji abin da Gwamnan Ribas yayi bayan Real Madrid sun yi nasara


Kungiyar Real Madrid ce ta lashe kofin Champions league na bana 2017


– Hakan ta sa Gwamna Nyesom Wike ya hada ‘yar liyafa


– Gwamna Wike da wasu ‘Yan PDP sun yi bikin murna




  • Real Madrid ta doke Juventus a wasan karshe na kofin Champions league
  • Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas yayi walima don murna
  • Gwamnan zai kuma bude makarantar koyon kwallo na Real Madrid


Babban Dan wasan Real Madrid watau Ronaldo ya zura kwallaye biyu a wasan su da Juventus a wasan karshe na makon. Juventus ta sha kashi ne a hannun Madrid da ci 4-1 a Birnin Cardiff wanda hakan ta sa Gwamna ya kira walima.




Gwamnan Jihar na Ribas ya hada walima domin Jama’a su taya sa murnar lashe wannan kofi. An ga Gwamnan tare da rigar Kungiyar Real Madrid da kuma mai dakin sa suna ta faman murna bayan Kungiyar ta doke Juventus ta ajiye tarihi.

Ku na sane cewa Real Madrid ta kara lashe kofin Nahiyar Turai na UEFA Champions league inda ta lallasa Zakarun Italiya. Dan wasa Ronaldo ne ya kara gamawa da kwallayen da su ka fi na kowa bayan ya jefa 2 a wasan karshe.





[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...