Sunday, June 4, 2017

2019: Arewa za ta tsaida shugaban kasa-Doyin Okupe





Idan Buhari ba ya nan, bai dace Osinbajo ya zarce ba… Inji Okupe



– Doyin Okupe yana nan kan bakan sa game da zaben


– Okupe yace ba a kyautawa ‘Yan Arewa idan Osinbajo ya zarce ba


– Dr. Okupe yace haka aka yi da Jonathan bayan rasuwar Shugaba ‘Yaradua



‘Dan Arewa zai tsaya takara a 2019 ba Osinbajo ba Inji Okupe


Okupe ya kara jaddada cewa Arewa ya dace ta tsaida dan takara idan Buhari ba ya nan. Na kusa da Shugaba Jonathan din yace ba ayi wa Arewa adalci ba. Yanzu haka dai Osinbajo ke rike da Najeriya bayan da Shugaba Buhari ya koma asibiti.

Babban mai ba shugaba Goodluck Jonathan shawara a baya ya kara magana game da zaben 2019 inda yace bai dace Farfesa Yemi Osinbajo ya zarce ba idan Shugaba Buhari ba zai tsaya ba ko wani abu ya same sa.

Dr. Doyin Okupe yace wasu ‘Yan Arewa na ganin cewa ba ayi masu daidai ba lokacin da Jonathan ya zarce bayan rasuwar Shugaban kasa Ummaru ‘Yaradua. Okupe yace duk da ba dokar da za ta hana Osinbajo tsayawa amma adalci shi ne ya ba Arewa wuri.

Ganin yadda Shugaban kasa Muhammadu Buhari ke fama da rashin lafiya kuma bai bayyana cewa zai tsaya takara ba. Tun kwanaki Doyin Okupe yace bai kamata kujerar ta bar Yankin Arewa ba.







No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...