Thursday, June 15, 2017

An koma saida dabinon da Saudi ta aikowa Najeriya sadaka




Abin kunya: Saudi ta aikowa Najeriya dabino sadaka amma an saida


  • Kasar Saudi ta aikowa Najeriya sadakar dabino na azumi
  • Sai ga shi yanzu ana saida wannan dabino a kasuwa
  • Ministar kasar da tayi alkawarin za a rabawa ‘yan gudun hijira




Wannan abin kunya sai ace da me yayi kama. Najeriya dai ta kara buga abin kunya a idon Duniya bayan an fara saida dabinon sadaka a kasuwa. An dai aikowa Najeriya sadaka amma an kai kasuwa domin a ci riba.

Kwanakin baya kun ji cewa Ofishin Jakadancin Saudiya a Najeriya ya bayyana cewa kasar ta aikowa Najeriya tulin dabino domin buda baki. Sai dai yanzu haka wannan dabino na yawo a kasuwa cikin Abuja ana saidawa.



Karamar Ministar harkokin kasar waje Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim tayi alkawari da fari cewa za a raba kayan ne musamman ga ‘Yan gudun Hijira da ke Yankin Arewa maso gabas sai dai ba haka abin ya kasance ba.

Gwamnatin Tarayya ta bakin Ma’aikatar harkokin kasar wajen ta ba Kasar Saudiya hakuri inda tace wasu bata-gari ne su ka yi gaba da dabinon bayan an kai inda ya kamata a raba su domin su samu abin Duniya.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...