Dole na mu yayi: ‘Yan
Kudu sun fito da ‘Yan takara a zaben 2019
– Inyamuran Najeriya sun fitar da
‘Dan takara a zabe mai zuwa
– Cikin wanda
ake nema su tsaya takara har da Patience Jonathan
– Gwamna Rochas
Okorocha yana cikin wannan jerin
Wata Kungiya ta Inyamamuran Duniya ta zabi ‘Yan
takaran ta a zabe mai zuwa. An yi wannan jawabi ne bayan wani taro a Garin Enugu kwanan nan. Inyamuarai sun tabbatar da cewa babu gudu ba ja da
baya a zaben shekarar 2019.
Yan Kudancin Najeriya sun fito da ‘Yan takara kusan 15 a zabe
mai zuwa daga ciki akwai matar tsohon shugaban kasa watau Patience Jonathan.
Inyamurai dai sun ce zabe mai zuwa ba abin da zai hana su harin kujerar Shugaban kasa.
Sauran dai wadanda ake sa rai su dare kujerar
shugaban kasar sun hada da tsofaffin Gwmanoni Orji Uzor Kalu, Peter Obi, da
Gwamna Rochas Okorocha, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Ike Ekweremadu
da dai sauran su.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment