Friday, June 30, 2017

Ayyiriri: Yau Dan wasa Lionel Messi zai yi aure



 Yau Dan wasan Duniya Messi zai zama Ango



  • Yau Juma’a ne auren Dan wasan Barcelona Lionel Messi
  • Tuni har Jama’a sun fara cika kauyen Dan wasan a Argentina
  • Messi ya gayyaci tsohon Dan wasan Real Madrid Di-Maria



A yau ne babban Dan wasan Duniya Messi zai shiga daga ciki. Lionel Messi zai auri sahibar sa mai suna Antonella Rocuzzo. Tauraron Dan Messi ya dade tare da wannan Budurwar ta sa tun su na kananan yara. 

A yau ne Dan wasa Lionel Messi na Barcelona zai zama Ango a Birnin Rosario da ke Kasar Argentina. Dan wasa Lionel Messi zai auri Budurwar sa da su kayi shekara da shekaru tare tun su na kanana Antonella Roccuzzo.




Tuni dai har Birnin Rosario ya cika makil wurin daurin auren da ba a taba yin irin sa ba cikin shekaru. Abokan wasan ‘Dan kwallon na Barcelona da sauran su sun fara hallara a jirgi. Messi ya gayyaci ‘Dan kasar sa kuma tsohon Dan wasan Real Madrid Angel Di-Maria.

Haka kuma kun ji cewa babban Dan wasan nan na Real Madrid Cristiano Ronaldo ya samu jarirai tagwaye masu suna Mateo da Eve.




[NAIJ Hausa]

Thursday, June 29, 2017

Yau Najeriya za ta fitar da doya kasar waje



Najeriya ta fara fitar da doya zuwa Kasar China


  • Yau Najeriya ta fara fitar da doya zuwa Kasar China
  • Duk Duniya babu inda ya kai Najeriya noman rogo da doya
  • Gwamnatin Shugaba Buhari ta dage wajen harkar noma



Hakika Shugaba Muhammadu Buhari ya dage wajen ganin an koma noma a kasar nan. Yanzu haka Kasar Najeriya za ta fara fitar da doya a yau dinnan da mu ke magana. Tuni kasashen China da sauran su suka nemi a kawo masu doya daga kasar nan.

Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta dage wajen harkar a kasar nan wanda yanzu har ta kai yau za a fara fita da doya zuwa kasar waje. Ministan gona na kasar Cif Audu Ogbeh ya tabbatar da wannan kamar yadda mu ka samu labari.

Kasar China watau Sin dai tayi odar wannan kaya wanda zai ba Najeriya damar samun kudin kasar waje. Duk Duniya babu inda ya kai Najeriya noman rogo da doya musamman ta bangaren Arewa maso tsakiya na kasar.

A bara an noma sama da ton miliyan biyu na shinkafa a Najeriya. Yanzu dai abin da Najeriya ta ke fitarwa ya fi karfin abin da ake shigo da shi wanda shi ne manufar Gwamnatin Shugaba Buhari.



[NAIJ Hausa] 


Wednesday, June 28, 2017

Jami'o'in da su ka kara kudin makaranta a Najeriya


 Talaka ya bani: Jami’o’i da dama sun kara kudin makaranta

 

– Ku na sane cewa Jami’o’i sun kara kudin makaranta a kasa


– Daga cikin wadanda su ka yi mugun kari akwai Jami’ar FUTA


– Majalisa ta nemi ayi mata bayanin dalilin wannan kari


– Kungiyar ASUU tace Gwamnatin Buhari tayi watsi da ilmi



Jami’o’i akalla 38 su ka kara kudin makaranta. Mun kawo maku jerin Makarantun da su ka kara kudin nasu. Jami'ar fasaha ta akure dai ta zabga kudi daga N14000 zuwa kimanin N84000. 

1.      Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya
2.      Jami’ar Legas ta UNILAG
3.      Jami’ar Nnamdi Arzikwe UNIZIK
4.      Jami’ar Bayero ta Kano
5.      Jami’ar Usman Danfodio ta Sokoto
6.      Jami’ar Abuja da ke Gwagwalada
7.      Jami’ar NOUN
8.      Jami’ar Benin ta UNIBEN
9.      Jami’ar fasaha ta Akure
10.  Jami’ar fasaha ta Minna
11.  Jami’ar Kalaba
12.  Kwalejin koyon karatu da ke Akoka
13.  Jami’ar Jihar Osun
14.  Makarantar koyon aiki da ke Ibadan
15.  Jami’ar Jihar Anambra
16.  Jami’ar Babangida da ke Lapai
17.  Jami’ar Afe Babalola
18.  Jami’ar Igbinedion
19.  Jami’ar Crowford
20.  Jami’ar Redeemers

Sauran Jami’o’in da su ka kare kudi kuma dai sun hada da:

21.  Jami’ar Jihar Filato
22.  Makarantar koyon aiki na Abiya
23.  Makarantar koyon aiki na Auchi
24.  Jami’ar fasaha ta Jihar Enugu
25.  Jami’ar Legas ta UNILAG
26.  Jami’ar Awolowo ta Ife
27.  Makarantar koyon aiki da ke Kwara
28.  Makarantar koyon aiki ta Abiyola
29.  Jami’ar Benson Idahosa
30.  Jami’ar Covenenat
31.  Makarantar koyon aiki ta LAUTECH
32.  Jami’ar koyon karatu Tai Solarin




[NAIJ Hausa]

Sunday, June 25, 2017

Sakon Shugaban Kasa Buhari na karamar Sallah




Sallar Idi: Sakon Shugaba Buhari ya kwantar da hankalin ‘Yan Najeriya

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aika sako ga mutanen Najeriya
  • Ana ma dai sa ran Shugaban kasar ya kusa dawowa Najeriya
  • Mun ji kishin-kishin din cewa dimuwa ta fara kama Shugaban kasar




Shugaba Buhari ya aiko sakon Sallah ga ‘Yan Najeriya ta bakin Garba Shehu. Shugaban Kasar yayi godiya inda ya nemi a zauna lafiya a Najeriya. Masu nazari kuma sun tabbatar da cewa muryar shugaban ce ba kage ba. Wannan dai ya sa hankalin da dama na kasar ya kwanta.

Yayin da wasu ke maganar cewa rashin lafiyar Shugaban kasa Muhammadu Buhari na kara tabarbarewa sai ga shi ya aiko sakon Sallah ga ‘Yan Najeriya inda yayi kira a cigaba da zama lafiya a kasa tare da addu’a domin sauke nauyin da ke kan Shugabannin.

Shugaban kasar dai ya godewa ‘Yan Najeriya game da irin addu’o’in da aka rika masa yayin da yake fama da jinya. Masu nazari dai sun ce ba shakka cewa muryar Shugaban kasar ce don kuwa ya taba abubuwan da su ke faruwa a kasa.


[NAIJ Hausa]

An yi wa Shugaba Buhari addu’a a Sallar Idi


Hudubar Idi: Limamin ABU yayi kira ga ‘Yan Najeriya


  • Babban Limamin masallacin Jami’ar A.B.U yayi kira ga ‘Yan kasa
  • Sheikh Salihu Abubakar ya nemi ‘Yan Najeriya su daina dogaro da Gwamnati
  • Malamin yayi wa Kasar Najeriya da sauran Jama’a addu’a



Sheikh Salihu Abubakar ya kira Jama’a su tashi tsaye wajen kawo gyara. A cewar babban Shehin ba dole Gwamnati ce za tayi gyara ba. Malamin yayi wa kasa da Shugaba Buhari addu’a. 

Babban Limamin masallacin Jami’ar A.B.U watau Ahmadu Bello Sheikh Salihu Santalma Abubakar yayi kira ga ‘Yan Najeriya da su tashi tsaye kuma su daina dogara ko-ca-kam kan Gwamnatin Kasar. Haka kuma  Malamin yayi wa Shugaban kasa da Jama’a duk addua.


Babban Limamin masallacin Jami’ar A.B.U yayi kira ga ‘Yan kasa


Shehin Malamin yayi kira da ‘Yan kasa su dage a duk matakin da su ke na kawo gyara. Sheikh S.S Abubakar ya nemi Jama’a da su kawo gyara domin za a tambaye su duk inda su ka samu kan su domin kawo gyara na gari a cikin al’umma.

Kun ji cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aiko sakon Sallah ga ‘Yan Najeriya ta bakin mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai Mallam Garba Shehu. Shugaban Kasar yayi godiya inda ya kuma nemi a zauna lafiya a Najeriya.


           




[NAIJ Hausa]

Friday, June 23, 2017

Najeriya za ta kere Amurka a wajen yawan Jama’a



Yawan mutanen Najeriya zai karu nan da 2050



  • Harsashe ya nuna cewa yawan mutanen Najeriya zai lula
  • A haka ma dai Najeriya ce ta 7 wajen yawa a Duniya
  • Zuwa shekarar 2050 kasar za ta kere Amurka
  • Kenan yawan 'Yan Najeriya zai zarce mutane Miliyan 300
  • Najeriya na da arziki amma 'Yan Najeriya na cikin talauci





Yawan mutanen Kasar Najeriya kara karuwa kurum yake yi. Nan da wani lokaci Najeriya za ta zama ta uku wajen adadin Jama’a. Kasar China da kuma India ne sahun gaba wajen yawan al’umma a Duniya. 

Wani harsashe da wata Hukuma da ke kula da yawan Jama’a na Duniya tayi ya nuna cewa Najeriya za ta kerewa Kasar Amurka wajen yawan mutane nan da shekarar 2050. Hakan na nufin Najeriya za ta zama ta uku wajen yawan Jama’a a kaf Duniya.






Zuwa wannan lokaci dai yawan haihuwar da ake samu a Nahiyar Afrika zai ribanya wanda ake samu a halin yanzu. Zuwa shekarar 2020 adadin Jama’an Duniya dai zai kusa Biliyan 10. Yanzu dai adadin mutanen Duniyar yak era mutum Biliyan 7.6.

Kasashe irin su Najeriya da China watau Sin, Indiya, Indonesiya, Fakistan da Amurka su na cikin wadanda su ka fi yawan al’umma a Duniya. Najeriya na fama da matsaloli daban-dabam irin na talauci, jahilci, kuncin rayuwa, yawan laifuffuka, ta'addanci da matsalar zamantakewa. 




[NAIJ Hausa]

Thursday, June 22, 2017

Laifin haraji: Wani babban Dan wasa zai wuce gidan yari?


An kama tsohon Dan wasan Real Madrid da laifin rashin biyan haraji


  • Dan wasan PSG Di-Maria bai biya wasu kudin haraji ba
  • Angel Di-Maria ya tabbatar da bakin sa cewa bai da gaskiya
  • Sai dai da wuya Di-Maria ya shiga gidan kurkuku wannan karo


Bayan Cristiano Ronaldo an kara samun wani Dan wasa da laifin haraji. Dan wasan gaba Di-Maria na Kasar Ajentina bai da gaskiya. Ta tabbata da bakin Dan wasan cewa bai biya wasu kudi ba lokacin yana wasa a Sifen. 

An kama tsohon Dan wasan gaban Real Madrid da Manchester United Angel Fabian Di-Maria da laifin rashin biyan kudin haraji a lokacin da yake kasar Sifen kamar yadda mu ke samun labari daga Jaridun Turai.

Di-Maria ya tabbatar da kan sa cewa akwai wasu kudi har na Dalar Euro Miliyan £1.14 da ya ki biya kamar yadda doka ta tanada. Hakan dai ta sa aka yanke masa daurin shekara daya a gidan maza. ‘Dan wasan ba zai yi zaman yari ba tun da wannan ne karo na farko da aka kama sa da laifi.

Ku na da labari cewa Dan wasa shi ma Cristiano Ronaldo na shirin barin Real Madrid bayan an fara zargin sa da kin biyan haraji. Shi ma tsohon Kocin na sa Jose Mourinho bai sha ba.



[NAIJ Hausa]


Dino Melaye zai bar Majalisa ba girma ba arziki


An kai mataki na gaba wajen shirin maido Sanata Dino Melaye gida



  • Maganar tsige Dino Melaye daga Majalisa na ta kara karfi
  • Sanatan na Jihar Kogi na cikin babban matsala a halin yanzu
  • Melaye dai yace Gwamnan Jihar sa da wannan danyen aiki


Shirin kiranye: Cikin Sanata Dino Melaye ya duri ruwa


Dama kuna da labari cewa Dino Melaye na cikin tsaka mai wuya. Mutanen mazabar sa na Yammacin Kogi na shirin yi masa kiranye. Idan hakan ya tabbata Sanatan zai bar Majalisa ba girma ba arziki. 

Sanata Dino Melaye na Yammacin Jihar Kogi ya tare su bayan da Hukumar zabe ta kasa watau INEC ta karbi takardun shaida na cewa mutanen mazabar na Jihar Kogi sun zabi a maido Sanatan da su ka zaba gida.




Dama kun dai ji cewa mutane 188,588 su ka sa hannu inda su ka nemi a maido Sanata Dino Melaye gida daga Majalisar Dattawa inda yake wakiltar mazabar sa ta Yammacin Kogi. Kawo yanzu an mikawa Shugaban Hukumar zabe na kasa wannan bayani a jiya.

Rikicin Gwaman Bello na Jihar da Sanata Dino Melaye ya kai inda ya kai. Sanatan ya zargi Gwamnan Jihar da hannu a cikin yunkurin da ‘yan mazabar sa ke yi na yi masa kiranye wanda yanzu maganar tayi nisa. A baya dai an san Sanatan da yawan shiga cikin rikici ko yanzu ya za a kare?

           
[NAIJ Hausa]

Wednesday, June 21, 2017

Babu maganar tursasawa Jama’a Musulunci a Najeriya


Gwamnatin Tarayya ta kauda zargi na yunkurin Musuluntar da Najeriya


  • Gwamnatin Tarayya ta kauda duk wani zargi game da maganar wasu Fastoci

  • Wasu na ganin akwai makarkashiya na tursasawa ‘Yan Najeriya Musulunci

  • Gwamnatin kasar dai ta yi watsi da wannan maganar kamar yadda za ku ji




Wasu na ikirarin cewa an soke ilmin addinin Kirista daga darussan Sakandare. Haka kuma ana yada cewa an saka larabci da ilmin addinin musulunci. Ma’aikatar ilmi dai ta wanke duk wannan zargi dalla-dalla.

Gwamnatin Tarayya ta musanya zargin da ke yawo na cewa an soke ilmin addinin Kirista daga darussan makaruntun Sakandare. Gaskiyar maganar dai ita ce tun lokacin tsohon Shugaba Jonathan aka fara wani garambawul a tsarin ilmin kasar.

Yanzu haka dai an maida darusan addinin musulunci da na kiristanci wuri guda inda kowane dalibi zai dauki wanda ya dace karkashin wani darasi na dabam. Haka kuma an kawo yaren Larabci tare da na Faransanci ga duk mai bukata amma babu dole a lamarin.

Bayan Kungiyar CAN ta Kiristoci, Fasto Johnson Solomon yace Gwamnatin Buhari na kokarin murkushe addinin Kiristanci a kasar nan. Faston yace an soke ilmin addinin Kirista daga darasin makarantu kuma aka bar na Arabi da Musulunci. Wannan magana dai ba daidai ba ce sam.

Idan ba ku manta ba a cikin kwanan nan ne aka kai wani mugun hari a Garin Mambila da ke Jihar Taraba inda aka kashe Fulani da dama bayan an kona gidajen su. Har yanzu Gwamnatin Jihar da ta Tarayya ba tayi wa kowa jaje ko ta’aziyar Allah ya kyauta ba.





[NAIJ Hausa]

Tuesday, June 20, 2017

Darikar Tijjaniyya da Shi’a duk abu daya ne – Dahiru Bauchi




Danjuma da Danjumai: ‘Yan Darika da ‘Yan Shi’a ‘Yan uwa ne Inji Shehun Tijjaniyya


  • Babban Shehin Darika Dahiru Bauchi yayi magana game da Shi’a
  • Shehun Darikar yace su da ‘Yan Shi’a ‘Yan uwan juna ne
  • Dahiru Bauchi yace sun yi tarayya da ‘Yan Shi’a wajen son Manzon Allah



Sheikh Dahiru Bauchi yace ba su fada da ‘Yan Shi’a. Shehin ya fadi haka ne yayin da aka kai masa ziyara. ‘Yan Shi’a da Dariku su na kaunar Manzo Inji Shehin. Wasu 'Yan Shi'a ne su ka kai masa ziyara a Kano.

Babban Shehin Darika Tijjaniyya Dahiru Usman Bauchi ya bayyana cewa ‘Yan tarika da ‘Yan Shi’a duk jirgi daya ne ya dauko su don kuwa sun yi tarayya wajen kaunar Manzon Allah Muhammadu SAW.

Wasu ‘Yan Kungiyar Shi’a ne dai su ka kai masa ziyara bayan ya kammala karatun tafsirin bana. Ya yabawa ‘Yan Shi’ar wanda yace duk sun hadu wajen soyayyar Manzon Allah da iyalan sa. Shehin dai ya yabawa wannan ziyara da aka kai masa a Kano.






[NAIJ Hausa]

Rashin lafiya: An yi wa Shugaban kasa aiki a Kasar Turai



Fadar Shugaban kasa ta tabbatar da cewa an yi wa Shugaba aiki a asibiti


  • Rashin lafiya ta tasa Shugaban kasar Benin a gaba
  • An yi wa Shugaban aiki a Birnin Faris
  • Shugaba Talon dai ya dade yana jinya 



Shugaba Partrice Talon na Benin na fama da rashin lafiya. Abin har ya kai an yi wa Shugaban aiki har sau biyu. Kusan wata guda kenan Shugaban kasar ba ya Gari. Haka dai shi ma Shugaba Buhari na Najeriya na kwance a Ingila.

Shugaba Partrice Talon na Kasar Benin na fama da rashin lafiya na kusan wata guda wanda har ta kai aka kai shi Birnin Faris domin ya ga Likita. Rahoto na zuwa cewa dai har ta kai an yi wa Shugaban aiki a jiki har sau biyu.


An dai shafe wata guda kenan Shugaban kasar na Benin na Kasar Faransa inda ake lura da shi. Fadar shugaban kasar da farko dai ta bayyana cewa ba shakka an yi shugaban aiki wanda kusan duk ana sa rai cewa an dace.

Kun ji cewa haka kuma a Najeriya Shugaba Buhari Muhammadu ya koma Asibiti a can Landan tun kwanaki. Farfesa Yemi Osinbajo ke rike ragamar kasar har lokacin da Ubangiji yayi shugaba Buhari ya dawo.





[NAIJ Hausa]

Monday, June 19, 2017

Kamfanin NNPC ya rage farashin mai


Labari da dumi-dumi: Farashin mai ya ragu a Najeriya – NNPC


 – Kamfanin man NNPC ya rage farashin man dizal da kaso mai tsoka


– Ana saida lita a kan kusan N300 wanda yanzu yayi kasa da N200


– Mai magana da bakin Kamfanin ya bayyana wannan cigaba da aka samu





  • Farashin man dizal ya ragu yanzu a Najeriya Inji kamfanin NNPC
  • An samu saukin kusan kashi 42 bisa 100 kan abin da ake saidawa a baya
  • Jama’a dai za su ji dadin wannan sauki da aka samu a fadin kasar


Masu motoci da Injin da ke amfani da man dizal za su yi murnar yadda aka rage kudin man daga N300 zuwa N175. Farashin litan man ba zai dai wuce N200 ba daga yanzu kamar yadda kamfanin NNPC ya bayyana.

Mai magana da bakin Kamfanin watau Udu Ughamadu ya bayyana wannan cigaba da aka samu jiya inda ya ke jawabin irin matakan da su ka dauka domin saumun sauki da arahar kayan a cikin kasar.

Ku na da labari cewa takin da Gwamnatin Tarayya  ke saidawa ya fara tsada. A wasu wuraren ma dai an fara boye takin na zamani. Manoma dai sun koka da yadda kudin takin ya tsula daga N5500 zuwa N6500 kwanan nan.



[NAIJ Hausa]

Sunday, June 18, 2017

Ikon Allah: Har da Patience Jonathan za a tsaya takara mai zuwa?



Dole na mu yayi: ‘Yan Kudu sun fito da ‘Yan takara a zaben 2019



– Inyamuran Najeriya sun fitar da ‘Dan takara a zabe mai zuwa


– Cikin wanda ake nema su tsaya takara har da Patience Jonathan


– Gwamna Rochas Okorocha yana cikin wannan jerin





Wata Kungiya ta Inyamamuran Duniya ta zabi ‘Yan takaran ta a zabe mai zuwa. An yi wannan jawabi ne bayan wani taro a Garin Enugu kwanan nan. Inyamuarai sun tabbatar da cewa babu gudu ba ja da baya a zaben shekarar 2019.

Yan Kudancin Najeriya sun fito da ‘Yan takara kusan 15 a zabe mai zuwa daga ciki akwai matar tsohon shugaban kasa watau Patience Jonathan. Inyamurai dai sun ce zabe mai zuwa ba abin da zai hana su harin kujerar Shugaban kasa. 

Sauran dai wadanda ake sa rai su dare kujerar shugaban kasar sun hada da tsofaffin Gwmanoni Orji Uzor Kalu, Peter Obi, da Gwamna Rochas Okorocha, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Ike Ekweremadu da dai sauran su.



[NAIJ Hausa]

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...