Sunday, April 30, 2017

Wasan dambe: Dan Najeriya ya gabje Klitschko

     
Abin alfahari: Dan Najeriya ya zama ‘Dan damben Duniya



 – Wani asalin dan Najeriya ya doke Klitschko a wasan dambe


– Yanzu haka ya karbi kambun damben Duniya


– Wladmir Klitschko ya sha kashi hannun Joshua






A wani wasan damben Duniya da aka yi a Kasar Ingila wani ainihin Dan Najeriya ne yayi nasara. Wannan dai abin farin ciki ne ga ‘Yan kasar da kuma daukacin bakaken Mutanen Afrika baki daya.

Anthony Joshua ya gabje Wladmir Klitschko a damben Duniyar da aka gwabza a filin wasa na Wembley da ke Birnin Landan inda mutane kusan 90, 000 su ka hallara gudun a gani a ba su labari.




Yanzu haka Joshua wanda asalin sa Dan kasar Najeriya ne ya karbe kanbun damben Duniyar na Heavyweight inda ya zama zakara bayan ya tika Zakaran Duniya Wladmir Klitschko da kasa a kusan zagaye na daf da karshe.

Anthony Joshua ya bayyana sirrin karfin da yake da shi yace ba zai rasa nasaba da sakwara da teba da sauran abincin 'Yan Najeriya ba.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...