Wednesday, April 26, 2017

Anya kalau: Yau ma Shugaban kasa bai halarci taro ba



Makonni kusan uku kenan ba a ga Buhari a taro ba
 

– Shugaban kasa Muhammadu Buhari bai halarci taron FEC ba


– Yanzu haka Osinbajo ke jan ragamar taron


Makonni uku kenan ba a ga shugaban kasar ba




Kusan makonni uku kenan ba a ga shugaba Buhari a taron Majalisar FEC da aka saba yi kowane mako ba. A halin yanzu haka Mataimakin shugaban kasa Farfesa YemiOsinbajo ke jan ragamar taron da ake yi na yau.

Wancan makom da ya wuce ba ayi taron ba sam, inda shugaban kasar yace lokacin an dawo daga hutun Easter a kurarren lokacin don haka aka bari sai Ministoci sun kintsa tukun ta bakin Malam Garba Shehu.

A makon baya ma dai shugaban kasa bai halarci taron ba inda Mataimakin sa ne ya ja ragamar. Ministan yada labarai yace ba wata matsala ce ta sa hakan ba illa-iyaka shugaban kasar ya ba Farfesa Yemi Osinbajo domin ya cigaba da wasu ayyuka na dabam.

Kwanaki aka kori wani Dan jarida daga Fadar Villa mai suna Olalekan Adetayo bayan Dan jaridar ya bayyana cewa shugaban kasar bai lafiya ba kuma a ganin sa. A taron na yau dai akwai wanda ta maye gurbin Babachir Lawal watau Dr. Habiba Lawal.

Yanzu haka mu ke jin cewa Ministan yada labarai na kasa Lai Mohammed yace shugaba Buhari na bukatar hutu don haka daga gida zai rika aiki. 



[NAIJ Hausa]

1 comment:

  1. Allah Ya kyauta Na gaba. Allah Ya qarawa shuwagabanin mu lafia da kuma Jagoranci Na alkhairi.

    ReplyDelete

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...