Tuesday, May 2, 2017

Dalilai 3 da su ka sa har Boko Haram tayi karfi


Abubuwa 3 da su ka sa ‘Yan Boko Haram su ka gagara


 


– Ana kan nasara wajen murkushe ‘Yan Kungiyar Boko Haram


– ‘Yan ta’addan sun kashe dinbin mutane a Yankin kasa da Nahiyar


– Ko ya aka yi suka yi wannan karfi haka a Duniya?





Wani Marubuci mai suna Theophilus Abbah ya zayyano dalilan da su ka sa Boko Haram tayi karfi. Duk da sakacin Hukuma akwai wasu dalilai da har su ka kawo Kungiyar tun farko. Na tsakuro daga ciki: 





1.      Jahilci da rashin aikin yi
Boko Haram tayi amfani da Jahilcin Matasa da kuma rashin sana’a inda aka nuna masu cewa aikin Allah su ke yi dama can ba su da wani aikin kuma ba su san Allah ba. Ko da wasu kadan cikin su na da karatu.


2.      Makamai
Boko Haram ta samu makudan kudi na sayen makamai da kuma makaman kan su daga wurare da dama. Ciki dai har da ta Arewacin Nahiyar bayan da Kasar Libya ta fadi daga hannun Marigayi Shugaba Moumar Gaddafi.

3.      Kashe makiya Kafirai
Ko da akwai rikicin siyasa tsakanin kungiyar sai dai sun yi tarayya wajen ganin bayan Kafirai da wadanda su ke kira Dagutu. Wajen su ko da an mutu wajen wannan gaba ta kai mutum.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...