Tuesday, April 25, 2017

Yadda fadar shugaban kasa tayi amai ta lashe

Yadda fadar shugaban kasa tayi amai ta lashe


– Kwanaki aka kori wani Dan jarida daga fadar shugaban kasa


– Jim kadan kuma sai ga shi an maido sa


– Hakan ya jawo alamar tambaya a kasar




Idan kuna biye za ku san cewa a farkon makon da ta wuce shugaban masu tsare shugaban kasa Bashir Abubakar ya kora wani Dan Jaridar Punch daga fadar shugaban kasar a cewar yayi wani rahoto game da lafiyar shugaban kasa Buhari.

Jim kadan kuma sai ga shi shugaban kasar ya bada umarni a maido Olalekan Adetayo ya cigaba da aikin sa. Shugaban kasar ya bayyana cewa Bashir Abubakar bai tuntube sa kafin ya dauki wannan mataki ba.

Shugaban kasar wanda tsohon Soja ne dai yana cikin abin da ya fara yi hawan sa mulki dawo da wani Dan jaridar kasar waje da aka kora a lokacin shugaba Jonathan ya cigaba da aikin sa domin nuna riddar sa zuwa Damukaradiyya.

Olalekan Adetayo ya bayyana cewa ana cewa ana neman sa dama dai yayi wuf ya kira mai magana da bakin shugaban kasar Femi Adesina. Nan gaba dai maganar za ta kara fitowa don kuwa Dan jaridar ya bayyana cewa shugaban kasar bai lafiya.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...