Tuesday, April 18, 2017

Ya za a kare tsakanin Buhari da Sanatoci



Yaushe za a kawo karshen rikicin Buhari da Sanatoci


– Ana ta samun rikici tsakanin shugaban kasa da ‘Yan majalisar Dattawa


An nada Kwamitin sulhu amma har yanzu ba a fara aiki ba


– Shugaban Majalisar yace yana bayan shugaban kasa





Kuna da labari cewa an nada kwamiti da zai zauna domin kawo karshen rikicin da ake ta fama tsakanin shugaban kasa Muhammadu Buahri da kuma ‘Yan majalisar Dattawar kasar.

Kwanaki aka yi ta samun takaddama tsakanin mutanen shugaban kasar da kuma Sanatocin Najeriya musamman game da shugabannin kwastam da kuma EFCC. Har dai ta kai Gwamnatin tarayya ta ke cewa za ta nemi ta shawo kan lamarin don yana ci mata tuwo a kwarya.




Shi dai shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki ya bayyana cewa babu wani rikici tsakanin su da shugaban kasa kai-tsaye inda ma ya nemi mutanen Najeriya su kara hakuri su kuma cigaba da marawa Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari baya yace shi ma yana goyon bayan ta. 

Shugaban kasa ya nada kwamiti domin sulhu da Majalisar daga ciki akwai dukkanin Ministocin kasar da su ka taba zama Sanatoci ko 'Yan Majalisar Tarayya a baya da kuma masu ba shugaban kasa shawara game da Majalisa Sai dai har zuwa yau Ranar Talata ba su fara wani zama ba.


[NAIJ Hausa]





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...