Yaushe za a kawo karshen
rikicin Buhari da Sanatoci
– Ana ta samun rikici tsakanin
shugaban kasa da ‘Yan majalisar Dattawa
– An nada Kwamitin sulhu amma
har yanzu ba a fara aiki ba
– Shugaban Majalisar yace yana
bayan shugaban kasa
Kuna
da labari cewa an nada kwamiti da zai zauna domin kawo karshen rikicin da ake
ta fama tsakanin shugaban kasa Muhammadu Buahri da kuma ‘Yan majalisar Dattawar
kasar.
Kwanaki
aka yi ta samun takaddama tsakanin mutanen shugaban kasar da kuma Sanatocin
Najeriya musamman game da shugabannin kwastam da kuma EFCC. Har dai ta kai
Gwamnatin tarayya ta ke cewa za ta nemi ta shawo kan lamarin don yana ci mata
tuwo a kwarya.
Shi
dai shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki ya bayyana cewa babu wani rikici
tsakanin su da shugaban kasa kai-tsaye inda ma ya nemi mutanen Najeriya su kara hakuri su
kuma cigaba da marawa Gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari baya yace shi ma
yana goyon bayan ta.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment