Friday, April 14, 2017

Tunawa da Sheikh Ja’afar Mahmud Adam


 
– A rana irin ta yau aka kashe Malam Ja’afar Mahmud Adam


– Wasu suka kashe babban Malamin yana tsakiyar sallar asuba


– Sheikh Ja’afar yana cikin manyan Malaman da aka yi a Arewa



Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam
A dalilin tunawa da Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam Daura da aka kashe shekaru 10 da suka wuce nayi wannan rubutu. An dai kashe Malam Ja’afar yayin da yake jagorantar sallar asuba a masallacin da yake Limanci.

Har yau dai ba a kama wadanda ke da hannu wajen kashe babban Malamin ba wanda ya ba addini rayuwar sa. An dai haifi Malam Ja’afar a Garin Daura a gidan Malamai, nan ya fara karatun addini daga nan ya koma Kasar Kano inda yayi almajiranci.

Daga nan ya kara karatun addini da boko a Garin Kano har ya samu nasara a gasar karatun Al-kur’ani. Daga nan Malamin ya samu wucewa Kasar Saudiyya inda ya Digiri a fannin Ilmin Al-Kur’ani a Jami’ar Madina.


Bayan ya kammala kuma ya zarce Kasar Sudan inda ya samu Digiri na biyu a fannin yaren larabci. A lokacin da aka kashe Sheikh Jafar yana digirin sa na uku a fannin addini Musulunci a Jami’ar Danfodiyo ta Sokoto.

Marigayi Ja’afar yana cikin malaman da suka kware wajen tafsirin Al-kur’ani da kuma iya bayani dalla-dalla ga Jama’a bisa koyarwar Sunnah ta Manzon tsira SAW. Malam Jafar ya koyar da al'umma ilmi da dama na Tauhidi da Hadisi da Sira da Fikihu na tsawon lokaci a fadin kasar nan. 

Allah ya jikan Malam Jafar Adam da Albani-Zaria ya karbi shahadar su. Ameen.



Muhammad Malumfashi ya rubuta wannan a shafin NAIJ Hausa jiya




No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...