Monday, April 17, 2017

Abin da ya sa Ahmed Musa ya rabu da matar sa



Dalilin da ya sa Dan wasa Ahmed Musa ya saki matar sa



– Babban Dan wasan gaban Najeriya Ahmed Musa ya saki matar sa


– Mataimakin Kyaftin din Najeriya ya nemi ya kara aure


– Matar sa tace sam ba za ta yarda ba


Ahmed Musa da Sahibar sa a da


Kuna da labarin cewa Dan wasan gaban nan na Najeriya da kuma kungiyar Leicester City ta Ingila yayi wa matar sa duka wanda daga baya ya karyata ya kuma ce zai maka gidan jaridar da su ka fara masa wannan kazafi a kotu.

Yanzu haka majiyar mu ta bayyana mana babban dalilin da ya sa Dan wasan ya rabu da uwar ‘ya ‘yan sa. Ahmed Musa dai yayi niyyar kara mata, wanda mai dakin sa fa ta tubure tace sam ba za ta yarda ba duk da cewa addini bai hana ba.



Juliet; Budurwar Tauraro Ahmed Musa

Abin ta kai har manya da iyaye su ka shigo cikin maganar domin a lallabi Jamila ta hakura da karin auren Mijin na ta amma abu ya faskara. Har Mahaifiyar Dan wasar ta je har Ingila domin ta shawo kan Sirikar ta amma fa tace sam ba za ta yarda ayi mata kishiya ba.

Hakan ta sa aka raba jiha tsakanin Ahmed din da Jamila uwar ‘ya ‘yan sa biyu bayan da ya tubure cewa sai ya kara aure ita ma ta cije.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...