Dalilin da ya sa Dan wasa Ahmed
Musa ya saki matar sa
– Babban Dan wasan gaban Najeriya Ahmed Musa ya saki matar sa
– Mataimakin Kyaftin din Najeriya
ya nemi ya kara aure
– Matar sa tace sam ba za ta yarda
ba
Ahmed Musa da Sahibar sa a da
Kuna da labarin cewa
Dan wasan gaban nan na Najeriya da kuma kungiyar Leicester City ta Ingila yayi
wa matar sa duka wanda daga baya ya karyata ya kuma ce zai maka gidan jaridar
da su ka fara masa wannan kazafi a kotu.
Yanzu
haka majiyar mu ta bayyana mana babban dalilin da ya sa Dan wasan ya rabu da
uwar ‘ya ‘yan sa. Ahmed Musa dai yayi niyyar kara mata, wanda mai dakin sa fa
ta tubure tace sam ba za ta yarda ba duk da cewa addini bai hana ba.
Juliet; Budurwar Tauraro Ahmed Musa
Abin
ta kai har manya da iyaye su ka shigo cikin maganar domin a lallabi Jamila ta
hakura da karin auren Mijin na ta amma abu ya faskara. Har Mahaifiyar Dan wasar
ta je har Ingila domin ta shawo kan Sirikar ta amma fa tace sam ba za ta yarda
ayi mata kishiya ba.
Hakan
ta sa aka raba jiha tsakanin Ahmed din da Jamila uwar ‘ya ‘yan sa biyu bayan da
ya tubure cewa sai ya kara aure ita ma ta cije.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment