Monday, April 3, 2017

Kare ya ceci mutane daga hannun Boko Haram


Ikon Allah: Wani kare ya hana a tada bam




kare yayi sanadiyar cecen rayuwar mutane masu dinbin yawa a Garin Borno inda ya hana wata yarinya tada bam a wani gidan biki

Sai ace ko karen nan yayi mutuwar shahada kenan inda ya rasa ran sa yana kokarin kare na Jama’a? Wannan kare dai yayi sanadin karin kwanan mutane masu yawa yayin da ya hana wata yariniya harba bam a wani gidan biki.

Mun samu labari cewa wannan kare na wani mai gida ne a kusa da inda wannan abu ya faru. Karen dai ya hana wata ‘yar yarinya kutsawa cikin Jama’a domin ta harba bam wanda da ya ga bayan mutane da dama a cikin wani gida da ake sha’anin biki.

Jami’an ‘Yan sanda su ka ce ko da karen ya hango wannan yarinya ta auka cikin Jama’a sai ya bi ta, nan fa aka yi ta kaya-kaya har bam din ya tashi, nan ne aka rasa wannan kare. Wannan abu dai ya faru ne a Garin Belbelo da ke Jihar Borno.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...