Tuesday, April 11, 2017

An kama masu bara fiye da 400 a Kano



Gwamnatin Jihar Kano ta damke mabarata da dama


– Gwamnatin Jihar Kano ta kama masu bara fiye da 400 a Jihar


– Hukumar Hisbah ce dai tayi wannan aiki a fadin Jihar


– Dama Sarki Muhammadu Sanusi II yace Arewacin Najeriya sun fi ko ina talauci



Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama masu bara da roko a Jihar Kano da dama cikin watan jiya da shekaran jiya kamar yadda mu ke samun labari yanzu haka. An dai kafa dokar da ta haramta bara a cikin Garin Kano.

Shugaban Hukumar Hisbah Malam Musa Tsangaya ya bayyanawa manema labarai wannan  kwanan nan. Tsangaya yace an kama masu bara a cikin Jihar wanda ya saba doka. Cikin dai wanda aka kama akwai manyan mutane kusan 200 yayin da sauran kuma dai kananan yara ne.

Mafi yawan wadanda aka kama dai ‘Yan asalin Jihar Kano ne yayin da sauran kuma su ka fito daga Jihohin Kaduna da Jigawa masu makwabtaka da Kano. Cikin wadanda aka kama dai har da maras hankali.

Kwanan nan Sarkin Kano ya bayyana cewa Arewacin Najeriya sun fi ko ina talauci a wani taro da aka yi a Kaduna. Akwai Almajirai sama da miliyan 3 a Jihar Kano kurum.





[NAIJ Hausa]

1 comment:

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...